Daga NASIR S. GWANGWAZO
Kimanin ɗalibai da ma’aikata sama da 90 da aka sace a Kwalejin Gwamnatin Tarayya da ke Yawuri a Jihar Kebbi sun shaƙi iskar ‘yanci bayan kwanaki 118.
Rahotanni daga jihar sun bayyana cewa, mahaifin ɗaya daga cikin ɗaliban da aka kama, wanda bai so a ambaci sunansa, shine ya tabbatarwa da Daily Trust hakan a daren nan, kamar yadda jaridar ta wallafa a shafinta.
Ƙarin bayani na nan tafe…