Month: December 2020

Kotun Kolin Amurka ta tabbatar wa Biden nasarar zabe

Kotun Kolin Amurka ta tabbatar wa Biden nasarar zabe

Daga Umar M. Gombe Kotun Koli na Amurka ta kawo karshen dogon takaddamar da ya dauki lokaci ana yi game da zaben shugaban kasa a kasar tun a watan Nuwamba, inda ta tabbatar wa dan takarar shugaban kasa na Democrat Joe Biden nasara. A cikin hukuncin da ta yi ba ranar Juma'a, kotun kolin ta kori karar da Shugaba Donald Trump ya shigar game da zargin tafka magudin zabe da aka yi a Pennsylvania da kuma jihohi uku na kasar. Jihohin hudun sun gabatar da shaidu gaban kotun, inda kuma suka bukaci alkalan kotun da su yi watsi da karar,…
Read More
El-Rufa’i ya sake killace kan sa bayan bullar cutar korona a gidan sa

El-Rufa’i ya sake killace kan sa bayan bullar cutar korona a gidan sa

Daga ABBA MUHAMMAD a Kaduna Sakamakon samun wasu daga cikin manyan ma'aikatan gwamnatin Jihar Kaduna da kuma mutum biyar daga cikin iyalin sa da kamuwa da cutar korona, Gwamna Nasiru Ahmad El-Rufa'i ya sake killace kan sa har sa har sai an yi masa gwaji. Gwamnan ya bayyana haka ne a daren Juma'a a cikin wani bidiyo mai tsawon minti 1:15. Wannan shi ne karo na biyu da ya killace kan sa bayan tabbatar da ci-gaba da hauhawar kamuwa da cutar a Jihar Kaduna da sauran jihohin Nijeriya. A bidiyon, gwamnan ya ce, "Ana ta ci gaba da kamuwa da…
Read More
Kotun Daukaka Kara ta tabbatar da hukuncin kisa ga Maryam Sanda

Kotun Daukaka Kara ta tabbatar da hukuncin kisa ga Maryam Sanda

Daga Umar Mohammed Gombe Kotun daukaka kara da ke zama a Abuja ta tabbatar da hukuncin kisan da aka yanke wa Maryam Sanda a kan kisan mijinta Bilyaminu Mohammed Bello da ta yi. A wani zama da kotun ta yi na mutum uku karkashin jagorancin Jastis Stephen Adah, a yau Juma'a da yamma, akan hukuncin da ta yanke, ya yi watsi da daukaka karar da Maryam Sanda ta shigar gaban kotun bisa rashin cancanta. A farkon wannan shekarar idan za a tuna, Mai Shari'a Yusuf Halliru na Babbar Kotu a Abuja da ke Maitama, ya yanke mata hukuncin kisa ta…
Read More
Bankin Zenith ne lambawan yanzu a bankunan Nijeriya

Bankin Zenith ne lambawan yanzu a bankunan Nijeriya

An zabi Bankin Zenith a matsayin banki na daya a jerin dukkan bankunan Nijeriya a yau. Hakan ta faru ne a wajen bikin bada kyaututtuka ga gwarzaye a bangaren aikin banki wanda mujallar The Banker da kamfanonin Finacial Times Group da ke London su ke shiryawa a kowace shekara. Bikin na bana, wanda aka gudanar a ran Laraba, sunan shi 'The Banker's Bank of the Year Awards 2020'. Da ma tun a farkon wannan shekarar mujallar da guruf din kamfanonin sun zabi bankin na Zenith a matsayin banki mafi daraja a kasar nan a bisa wani sikeli da su ka…
Read More
Darajar naira ta daga, ta koma N470 a kan dala 1 a kasuwar ‘yan canji

Darajar naira ta daga, ta koma N470 a kan dala 1 a kasuwar ‘yan canji

DAGA IRO MAMMAN Darajar naira ta karu a cikin wannan makon bayan ta samu mako biyu cikin karaya idan an canza ta da dala a kasuwar 'yan canji. A ranar Laraba ta samu karin N20, ta koma N470 a kan dala 1. Kafin wannan lokaci, naira ta karye da N30 a kan dala, domin canjin ta a kasuwa ya tashi sosai zuwa N500 a kan dala 1 daga ranar Litinin, 30 ga Nuwamba zuwa N470 a dala 1 a ranar Juma'a, 20 ga Nuwamba, 2020. To amma sababbin ka'idojin da Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya fito da su a ranar Litinin,…
Read More