Month: January 2021

Zamfara: Majalisa ta buƙaci Matawalle ya ɗauki mataki kan kuɗaɗen fansho

Zamfara: Majalisa ta buƙaci Matawalle ya ɗauki mataki kan kuɗaɗen fansho

Daga UMAR M. GOMBE Majalisar Dokokin Jihar Zamfara ta yi kira ga gwamnan jihar Bello Matawalle, da ya yi amfani da kuɗaɗen fansho Naira miliyan 500 da ke ɓoye a banki an rasa mai su wajen biyan ma'aikatan gwamnatin jihar da suka yi murabus haƙƙoƙinsu. Kazalika, majalisar ta buƙaci Gwamnan da ya nemi ganawa da Babban Lauyan Gwamnatin Tarayya kuma Ministan Shari'a, da kuma Babban Daraktan Hukumar Fansho ta Ƙasa domin tattauna yadda za a yi a biya ma'aikatan gwamnati a jihar abin da suka tara a can baya. A cewar Majalisar, "Wannan na daga cikin matsayar da ta cim…
Read More
Wataƙila cutar korona ta zama silar hana attajirai zuwa asibiti a ƙetare – Ume

Wataƙila cutar korona ta zama silar hana attajirai zuwa asibiti a ƙetare – Ume

Daga WAKILIN MU Wani Babban Lauyan Nijeriya kuma tsohon Babban Lauyan Jihar Imo, Chukwuma-Machukwu Ume ya ce, annobar korona ta ɗan taki wani matsayi na a yaba mata saboda tasirin da ta yi na kusa kawo ƙarshen bulaguron da wasu masu ƙumbar susa kan yi zuwa ƙasashen ƙetare don jinya. Ume ya ce, duba da yadda annobar ke ta yaɗuwa kamar wutar daji, hakan zai tilasta wa shugabannin siyasar Nijeriya gina manya asibitoci masu inganci kwatankwacin na sauran ƙasashen duniya da suka cigaba don kula da lafiyar al'umma. Waɗannan bayanai da Ume ya yi, suna ƙunshe ne cikin wata takarda…
Read More
Ina za a samu hoton Narambaɗa?

Ina za a samu hoton Narambaɗa?

Daga IBRAHIM SHEME Malam Ibrahim Buhari Maidangwale Abdulƙadiri Tubali, wanda aka fi sani da Ibrahim Narambaɗa, fitaccen makaɗin Hausa ne wanda ya rayu a tsakanin wajajen 1890 da Disamba, 1963. Ya yi waƙoƙi masu tarin yawa inda ya wasa sarakuna a ƙasashen Hausa da dama, irin su Zamfara da Maraɗi da Zazzau. Duk da yake a fagen waƙar sarauta ya fi yin fice, ya yi waƙoƙin noma da na ma'aikata (alƙalai) da na 'yan siyasa irin su Sardauna Ahmadu Bello da na sha'awa (misali waƙar 'Dokin Iska Ɗanhilinge'). An yi ittifaƙi da cewa ya na da zurfin basira, ta yadda…
Read More
Buhari ya sabunta rijistarsa ta zama a APC

Buhari ya sabunta rijistarsa ta zama a APC

Daga FATUHU MUSTAPHA A ranar Asabar da ta gabata Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya sabunta rijistarsa ta zama cikakken dan jam'iyyarsu ta APC, a mahaifarsa Daura da ke jihar Katsina. Tare da kira ga daukacin shugabannin jam'iyyar da karfafa kwazo wajen tabbatar da APC ta samu karin tagomashi a matakin farko. Buhari ya yi wannan kira ne a lokacin da ya karbi bakuncin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Ahmed Lawan da wasu gwamnoni hada da wasu 'ya'yan jam'iyyar APC a garin Daura, jim kadan bayan ya kammala sabunta rijistarsa ta jam'iyya a Gundumar Sarkin Yara. A wata sanarwa da mai magana…
Read More
Rattaba wa dokar NOUN hannu da na yi ya haifar wa dalibanta samun tagomashi – Buhari

Rattaba wa dokar NOUN hannu da na yi ya haifar wa dalibanta samun tagomashi – Buhari

Daga AISHA ASAS Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya bayyana cewa, rattaba hannu da ya yi a dokar Budaddiyar Jami'ar Nijeriya (NOUN) da aka yi wa gyaran fuska, ya haifar wa jami'ar da ɗalibanta samun tagomashi a kasa. Shugaban ya bayyana haka ne yayin bikin yaye daliban jami'ar karo na 9 da na 10 da aka hade wuri guda wanda ya gudana ta bidiyo a ranar Asabar da ta gabata. Da yake jawabi yayin bikin ta bakin wakilinsa Mataimakin Sakataren Hukumar Kula da Jami'o'i ta Kasa, Ramon Yusuf, Buhari ya ce, "Budaddiyar Jami'ar tana sauke nauyin da ya rataya a kanta…
Read More
Cutar Korona: Za a tabbatar da kiyaye dokokin kariya a Abuja – Minista

Cutar Korona: Za a tabbatar da kiyaye dokokin kariya a Abuja – Minista

Daga WAKILINMU Hukumar Birnin Tarayya, Abuja ta ce, za ta tabbatar da an bi dokokin yaki da Cutar Korona na 2021 kamar yadda Kwamitin Shugaban Kasa Kan Yaki da Cutar Korona ya shimfida. Hukumar ta bayyana haka ne a wajen wani taron masu fada a ji da ya gudana a karkashin jagorancin Ministan Abuja, Malam Muhammad Musa Bello, a Juma'ar da ta gabata a Abuja. Da yake jawabi yayin taron, Ministan Abuja ya ce, "Za a kara himma wajen wayar da kan mazauna Abuja game da kiyaye dokokin yaki da Cutar Korona, tare da tabbatar da an hukunta duk wanda…
Read More
Bauchi: Daliban makarantun kudi na iya neman gurbin karatu a makarantun gwamnati – Tilde

Bauchi: Daliban makarantun kudi na iya neman gurbin karatu a makarantun gwamnati – Tilde

Daga FATUHU MUSTAPHA Ma'aikatar Ilimi ta Jihar Bauchi ta bayyana cewa, dalibai daga makarantun sakandare masu zaman kansu a jihar na iya neman gurbin karatu a makarantun gwamnatin jihar don shiga aji hudu (SS1). Kwamishinan Ilimi na Jihar, Dr. Aliyu I. Tilde ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a wannan Asabar. A cewar kwamishinan, "Mun fahimci cewa iyaye kalilan ne da 'ya'yansu ke tafiya makarantun kudi ke da masaniyar cewa 'ya'yansu na da damar neman gurbin karatu a makarantun sakandaren gwamnatin jihar don shiga aji hudu ta hanyar amfani da sakamakonsu na BECE." Ya ci gaba…
Read More
Cutar Korona: Mutum 27 sun mutu a tsakanin sa’o’i 24 a Nijeriya

Cutar Korona: Mutum 27 sun mutu a tsakanin sa’o’i 24 a Nijeriya

Daga UMAR M. GOMBE Cibiyar Dakile Yaduwar Cututtuka ta Kasa (NCDC) ta bayyana cewa, an samu rasuwar mutum 27 cikin sa'o'i 24 a fadin kasa sakamakon Cutar Korona. Cibiyar ta sanar da hakan ne a shafinta na intanet a Juma'ar da ta gabata, inda ta ce kawo yanzu adadin wadanda suka mutu a fadin kasa a dalilin korona ya cilla zuwa mutum 1,557. Kazalika, NCDC ta sanar an samu karin mutum 1,114 da suka harbu da cutar ta korona a fadin kasa. Wanda a cewarta, "Ya zuwa yanzu mutum 128,674 ne aka tabbatar sun kamu da cutar a fadin kasa."…
Read More
NUJ ta yi rashi a Binuwai

NUJ ta yi rashi a Binuwai

Daga AISHA ASAS Allah Ya yi wa Shugabar Kungiyar 'Yan Jarida ta Jihar Benue, Comrade Victoria Asher, rasuwa. Asher ta rasu ne bayan da aka yi mata aiki ta haifi tagwaye. A sanarwar da sakataren NUJ na jihar, Moses Akarhan, ya fitar a wannan Asabar din, ta nuna Asher ta rasu ne da misalin karfe 8 na safiyar Asabar a asibitin FMC da ke Makurdi bayan da aka yi mata aiki. Tuni dai gwamnan jihar Benue, Samuel Ortom, ya bayyana kaduwarsa game da rasuwar. Kana ya yi fatan Allah ya bai wa iyalan marigayiyar juriya da danganar rashin.
Read More
Buhari ya tafi Daura don sabunta rijistar zama dan APC

Buhari ya tafi Daura don sabunta rijistar zama dan APC

Daga FATUHU MUSTAPHA Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya yi tafiya zuwa mahaifarsa Daura, da ke jihar Katsina. Buhari ya yi wannan tafiya ne a Juma'ar da ta gabata domin sabunta rajistar zama mamba a jam'iyyar APC wanda jam'iyyar ke shirin somawa a fadin kasa. Gwamnan jihar Katsina, Aminu Bello Masara da Mataimakin Kakin Majalisar Dokokin jihar da sauransu, na daga cikin wadanda suka tarbi shugaban bayan da ya isa Babban Filin Jirgin Sama na Umaru Musa Yar’Adua da ke Katsina. A bangare guda, Sarkin Daura Alhaji Faruk Umar Faruk, ya jagoranci dakatai da sauran su, inda suka ziyarci Buhari a…
Read More