Month: February 2021

Ɗanwaire gwanki sha bara (1924)

Ɗanwaire gwanki sha bara (1924)

Daga FATUHU MUSTAPHA Babu takamaiman ko wacce shekara aka haifi Ɗanwaire, sai dai an bayyana cewa asalin sunan sa Muhammadu. Iyayen sa da alama dai Fulani ne, kuma asalain sa shi da mutumin Kano ne. an haife shi a garin Waire da ke ƙasar Bichi a yanzu. Babu kuma wani cikakken bayani akan ko wane irin nau’in Fulani ne. A taƙaice dai, asali da tasowar Ɗanwaire abu ne da har yau masana basu samu wani cikakken bayani a ka ba. Amma dai an fara jin ɗuriyar Ɗanwaire ne a zamanin sarkin Kano Bello1882 – 1893. Hakan na nuni da cewa…
Read More
An daina kishi na faɗan baki, sai na ƙwandala – Khadija Mahuta

An daina kishi na faɗan baki, sai na ƙwandala – Khadija Mahuta

Hajiya Khadija Abdulrasheed Mahuta mace ce wadda ya kamata mata su yi koyi da ita, kasancewar ta jaruma kuma tsayayya, sannan da ta san ciwon kan ta. Ta kasance cikin jerin mata da su ke tauna taura biyu a lokaci guda. Ma’ana, mace ce wadda ba ta zauna ba don jiran sai wani ya samo ya kawo mata, a’a, ta tashi tsaye ne haiƙan wajen rufa wa kan ta asiri. Wakiliyar Manhaja ta tattauna da ita inda ta bayyana wa masu karatu rayuwar ta wadda za ta iya zama makaranta ga mata. Daga AISHA ASAS Masu karatu za su so…
Read More
Za mu yi maganin ‘yan fashi da masu tada ƙayar-baya, cewar Buhari

Za mu yi maganin ‘yan fashi da masu tada ƙayar-baya, cewar Buhari

Daga FATUHU MUSTAPHA Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari, yayi gargaɗin cewa babu wani sassauci game da matakan da gwamnati ta shirya ɗauka na neman kawar da matsalolin 'yan fashi da masu tada ƙayar-baya da sauran manyan laifuka da suka addabi al'umma a faɗin ƙasa. Buhari ya yi wannan gargaɗi ne ta bakin Shugaban Ma'aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Farfesa Ibrahim Gambari, yayin wani taro kan sha'anin tsaro wanda gwamnonin Arewa da sarakunan gargajiya suka gudanar a Jihar Kaduna. Buhari ya yarda cewa lallai Nijeriya na fama da matsalolin tsaro, amma cewa ya buƙaci sabbin shugabannin tsaro da samar da sabbin dabaru kuma…
Read More
Legas: Hukumar Kwastam ta kama taramo katan 554

Legas: Hukumar Kwastam ta kama taramo katan 554

Daga AISHA ASAS Ofishin Hukumar Yaƙi da Fasa-ƙwauri ta Nijeriya (NCS) da ke Apapa a Legas, ya ce ya kama wani kwantena mai lamba 1793504 wanda aka yi amannar tais (tiles) ne aka ɗauko, amma bayan da aka zurfafa bincike sai aka gano katan-katan na ƙwayar taramo guda 554 maƙare a cikin sunduƙin. Da yake yi wa manema labarai bayani a ranar Alhamis da ta gabata Shugaban Hukumar na Apapa, Controller Malanta Yusuf, ya ce kimanin makonni uku da kama aiki a Apapa, sun yi nasarar kama sunduƙai da dama ɗauke da kayayyakin da aka haramta shigo da su cikin…
Read More
Bauchi: Za a kammala sansanin alhazai kafin Hajjin bana

Bauchi: Za a kammala sansanin alhazai kafin Hajjin bana

Daga WAKILIN MU Gwamnatin Jihar Bauchi ta bada tabbacin cewa, za ta kammala aikin gina katafaren sansanin alhazai na ƙasa-da-ƙasa da ta sa a gaba kafin aikin Hajjin 2021 ya kankama. Sakataren Hukumar Kula da Jin Daɗin Alhazai na jihar, Alhaji Abubakar Babangida Tafida (Tafidan Giade), shi ne ya bada wannan tabbaci yayin ziyayar da ya kai a sansanin a ranar Alhamis da ta gabata don gane wa idanunsa yadda aiki ke gudana. Jim kaɗan bayan kammala ziyarar, Babangida Tafida ya shaida wa manema labarai cewa, aikin sansanin alhazan na ɗaya daga cikin ƙudurorin gwamnatin Gwamna Bala Abdulkadir Muhammad na…
Read More
‘Yan bindiga sun sace ɗalibai mata kimanin 300 a Zamfara

‘Yan bindiga sun sace ɗalibai mata kimanin 300 a Zamfara

Daga FATUHU MUSTAPHA Rahotanni daga Jihar Zamfara, sun nuna cewa 'yan bindiga sun sace ɗalibai mata kusan su 300 a Makarantar Sakandaren Gwamnati (GSS) Jangeɓe, da ke yankin ƙaramar hukumar Talata-Mafara a jihar, a tsakar daren Juma'a. Kwamishinan Labarai na jihar, Malam Suleiman Tunau Anka, ya tabbatar wa manema labarai faruwar haka, inda ya ce 'yan bindiga sun shiga makatar ne da misalin ƙarfe 1 na tsakar daren Juma'a suka kwashi ɗalibai. Sai dai Anka bai faɗi adadin ɗaliban da lamarin ya shafa ba. Wannan na faruwa a daidai lokacin da Gwamnan jihar Zamfara Bello Matawalle, ya yi kira ga…
Read More
EFCC ta yi sabon shugaba

EFCC ta yi sabon shugaba

Daga FATUHU MUSTAPHA A Larabar da ta gabata Majalisar Dattawan Nijeriya ta tabbatar da Abdulrasheed Bawa a matsayin sabon Shugaban Hukumar Yaƙi da yi wa Tattalin Arziki Zagon Ƙasa da Zambar Kuɗaɗe (EFCC). Sanatocin sun shafe sa’o’i biyu suna tantance Bawa kafin daga bisani suka tabbatar da shi a sabon matsayin nasa. Yayin da ake tantance shi, Bawa ya bai wa majalisar tabbacin cewa zai yi aiki tukuru don gyara wa hukumar zama ta hanyar inganta harkokinta kafin ƙarewar wa’adin jagorancinsa. Bawa ya ce zai yi aiki tare da waɗanda suka dace a sassan duniya domin tabbatar da Nijeriya ta…
Read More
Bello ya rattaba hannu a wasu sabbin dokokin jiharsa

Bello ya rattaba hannu a wasu sabbin dokokin jiharsa

Daga AISHA ASAS Gwamnan jihar Neja, Abubakar Sani Bello, ya sanya wa wasu sabbin dokoki guda biyu hannu. Dokokin su ne, dokar gudanar da binciken sanin lafiyar masu shirin yin aure kafin ƙulla aure da kuma dokar haramta tada hankalin jama'a da abin da ya jiɓanci haka. Taron sanya wa dokokin hannu ya gudana ne a Fadar Gwamnatin Jihar da ke Minna. Da yake jawabi bayan kammala sanya wa dokokin hannu, Gwama Bello ya bayyana dokokin a matsayin masu muhimmancin gaske. Bello ya yaba wa Majalisar Dokokin jihar bisa ƙoƙarin da ta yi wajen nazarin dokokin yadda ya dace har…
Read More
Myanmar: An yi arangama tsakanin magoya bayan sojoji da ɓangaren Suu Kyi

Myanmar: An yi arangama tsakanin magoya bayan sojoji da ɓangaren Suu Kyi

Rahotanni daga Ƙasar Myanmar sun nuna cewa, magoya bayan sojin da suka yi juyin mulki a ƙasar sun yi arangama da masu adawa da kifar da gwamnatin Aung San Suu Kyi a birnin Yangon, yayin da hukumomi suka daƙile ɗalibai a makarantunsu don hana su zanga-zanga. Tun lokacin da sojoji suka yi juyin mulki a ranar 1 ga Fabairu, tare da tsare Suu Kyi, ƙasar ta tsunduma cikin tashin hankali. Kimanin makonni uku kenan da ake gudanar da zanga-zanga a kowacce rana da kuma yajin aiki a ƙasar. Sai dai ‘yan sanda sun rufe ƙofofin makarantun da nufin hana ɗarruruwan…
Read More
FIAN ta nuna takaicinta kan yadda ƙungiyoyi kan gaza kula da ‘yanwasa

FIAN ta nuna takaicinta kan yadda ƙungiyoyi kan gaza kula da ‘yanwasa

Ƙungiyar Masu Shiga-tskanin Harkokin Ƙwallon Kafa ta Kasa (FIAN), ta nuna damuwarta kan yadda masu ruwa da tsaki kan harkokin ƙwallon ƙafa ba su ɗaukar lamarin 'yan ƙwallon da muhimmanci wajen biyan albashinsu da alawus-alawus da makamantansu yadda ya dace. Shugaban FIAN na ƙasa, Ayodele Thomas, ya nuna damuwarsa kan yadda masu ƙungiyoyin ƙwallon ƙafa suke nuna halin ko-in-kula wajen kula da sha'anin 'yan wasansu yadda ya kamata. Da yake zantawa da manema labarai, Thomas ya ce abin takaici ne yadda masu kulob-kulob kan gaza wajen lura da 'yan ƙwallonsu bilhaƙki. Ya ce kamata ya yi kafin ƙungiya ta ɗauki…
Read More