Month: May 2021

Me ya kawo rabuwar auren Sani Danja da Mansurah Isah?

Me ya kawo rabuwar auren Sani Danja da Mansurah Isah?

Daga MUKHTAR YAKUBU, a Kano A 'yan kwanakin nan babu abin da ya fi ɗaukar hankalin mutane kamar labarin rabuwar auren Sani Danja da Matarsa Mansurah Isah. Labarin dai ya fara ne tun daga ranar Larabar da ta gabata, in da ita Mansurah ta bada sanarwa a shafinta na Instagram cewa ba su tare da mijinta Sani Danja. To sai dai ba ta yi wani ƙarin bayani ba, sannan kuma bayan ɗan wani lokaci da saka labarin sai ta yi sauri da goge shi. Bayan wannan kuma ba ta ƙara cewa komai ba a kan lamarin. Wakilinmu ya yi ƙoƙarin…
Read More
Rasuwar Attahiru ta hana murnar kisan Shekau

Rasuwar Attahiru ta hana murnar kisan Shekau

*Har yanzu rundunar sojan Nijeriya na ci gaba da taka-tsantsan*Shin ko Nijeriya za ta amfana da nasarar ISWA kan Boko Haram?*Janar Yahaya: Wane ne wanda Buhari ya saka magajin Attahiru? Daga NASIR S. GWANGWAZO, a Abuja A ranar Alhamis, 27 ga Mayu, 2021, rahotanni suka fantsama a cikin Nijeriya da ƙasashen duniya cewa, ɗaya da daga cikin waɗanda Nijeriya da Amurka ke kallo a matsayin manyan maƙiyanta kuma jagoran ƙungiyar masu tayar da ƙayar baya da aka fi sani da Boko Haram, wato Abubakar Shekau, ya rasa ransa a wani artabu tsakanin mabiyansa da mambobin ɗaya ƙungiyar ita ma mai…
Read More
Zuwa ga ɗan uwa mai nufin ƙarin aure

Zuwa ga ɗan uwa mai nufin ƙarin aure

Daga AMINA YUSUF ALI Assalamu alaikum wa rahmatullah. Masu karatu sannunku da jimirin karatun shafinmu na zamantakewa daga jaridarku mai farin jini ta Manhaja. Ina muku godiya da fatan alkhairi, kamar yadda koyaushe kuke yi min ta hanyar kiran waya ko saƙon tes. Rubutun wannan mako dai na maza ne. Za mu yi magana a kan matakan da ya kamata yan uwa maza su ɗauka yayin da suke da nufin ƙaro aure. Ko kuma gwari-gwari a ce ƙaro mata daga ɗaya zuwa biyu, har ma sama da haka. Maza da yawa suna kokawa a kan yadda matansu na gida ke…
Read More
Hana kiwo a Kudu da raba kan Nijeriya

Hana kiwo a Kudu da raba kan Nijeriya

A makon nan ne Ƙungiyar Dattawan Arewacin Nijeriya (NEF) ta mayar wa ƙungiyar gwamnonin kudancin ƙasar nan da martanin cewa, su na gina mutanen da ke da tsananin nuna ƙabilanci da kuma ɓuya a bayan su suna tinzira jamaar su domin raba kan al'ummar ƙasa, wadda sanarwar hakan ke ɗauke da sa hannun Kakakin ƙungiyar, Dr. Hakeem Baba-Ahmed, da suka zargi gwamnonin da suka yi rantsuwar kare kundin tsarin mulki da taimaka wa masu fafutukar raba kan ƙasa da al'umma baki ɗaya. Ƙungiyar Dattawan Arewan ta bayyana matakin da gwamnonin kudancin ƙasar suka ɗauka na hana yawon kiwo a matsayin…
Read More
Lai ga ‘yan Nijeriya: Ƙasa na cikin aminci, babu buƙatar tada hankula

Lai ga ‘yan Nijeriya: Ƙasa na cikin aminci, babu buƙatar tada hankula

Daga WAKILINMU Minista Labarai da Al'adu, Alhaji Lai Mohammed, ya bai wa 'yan Nijeriya tabbacin cewa duk da matsalolin tsaron da ƙasa ke fuskanta, Nijeriya na cikin aminci ƙarƙashin gwamnatin Buhari. Da wannan ministan ya yi kira ga 'yan Nijeriya da kada su ji ɗar game da yanayi mara kyau da hasashen masu hasashe ke dangana ƙasar da shi. Lai ya faɗi haka ne a lokacin da ya karɓi baƙuncin Oluyin na Iyin-Ekiti, Sarki Adeola Adeniyi Ajakaiye da tawagarsa a Alhamis a ofishinsa da ke Abuja. A cewarsa, "Duk da ƙalubalan tsaron da ake fuskanta, ina so in yi amfani…
Read More
Buhari ya naɗa Yahaya a matsayin magajin Attahiru

Buhari ya naɗa Yahaya a matsayin magajin Attahiru

Daga BASHIR ISAH Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari, ya naɗa Major General Farouk Yahaya a matsayin sabon Shugaban Rundunar Sojojin Nijeriya. Kafin naɗin nasa, Major General Yahaya babban jami'i ne mai kula da ɓangare na 1 na rundunar sojojin Nijeriya, haka nan shi ne shugaban rundunar shirin Operation HADIN KAI mai yaƙi da ta'addanci a yankin Arewa-maso-gabas. Cikin sanarwar da ya fitar a Alhamis, Daraktan riƙo na sashen labarun rundunar, Brigadier General Onyema Nwachuku, ya buƙaci kafafen yaɗa labarai da su yaɗa wannan bayani domin sanar da 'yan ƙasa halin da ake ciki. Da wannan naɗin, ya tabbata cewa Major General…
Read More
Hajjin 2021: Za a soma yi wa maniyyatan Abuja rigakafin korona kashi na biyu

Hajjin 2021: Za a soma yi wa maniyyatan Abuja rigakafin korona kashi na biyu

Daga AISHA ASAS Hukumar Birnin Tarayya (FCTA) ta bayyana cewa za a soma yi wa maniyyatan Abuja allurar rigakafin cutar korona kashi na biyu ya zuwa Litinin, 31 ga Mayu, 2021. Mai magana da yawun hukumar, Muhammad Lawal, ya ce Daraktan Hukumar Kula da Sha'anin Maniyyata na birnin, Malam Muhammad Nasiru DanMalam, shi ne ya bada tabbacin hakan tare da cewa hukumar Abuja na yin dukkan mai yiwuwa domin ganin maniyyatan yankin sun cika duka sharuɗɗan Hajjin bana. Daraktan ya ce domin cim ma wannan ƙudiri, Sakatariyar Lafiya ta Abuja ta tanadi wadataccen rigakafin korona wanda za a yi wa…
Read More
Tunanin lamurra sun daidaita a Nijeriya yaudarar kai ne kawai – Sultan

Tunanin lamurra sun daidaita a Nijeriya yaudarar kai ne kawai – Sultan

Daga UMAR M. GOMBE Sultan na Sakkwato, Muhammad Sa’ad Abubakar, ya ce kada 'yan Nijeriya su yaudari kansu kan cewa lamurra sun daidaita a Nijeriya. Basaraken ya bayyana haka ne a wajen babban taro ka sha'anin tsaron ƙasa a Larabar da ta gabata a Abuja. Sultan ya ce, "Kada mu yaudari kanmu cewa abubuwan sun daidaita, lamurra sun taɓarɓare. Mun san da haka kuma mun gani. " Wasunmu, mun ga tasku a rayuwa. Yanzu kuwa abubuwa sun yi matuƙar dagulewa. Ba tare da wahalar da tunani ba, za a fahimci cewa Nijeriya na cikin hali mara daɗi kuma gaskiyar kenan."…
Read More
Inugu: ‘Yan bindiga sun sake ƙona ofishin ‘yan sanda, mutum 5 sun mutu

Inugu: ‘Yan bindiga sun sake ƙona ofishin ‘yan sanda, mutum 5 sun mutu

Daga UMAR M. GOMBE A safiyar Talata wasu 'yan bindiga suka kai wa ofishin 'yan sanda hari a Iwollo Oghe da ke yankin ƙaramar hukumar Ezeagu a jihar Inugu, inda suka ƙona ofishin ta hanyar banka masa wuta. Yayin harin, an yi zargin wasu mutum biyar sun halaka, ciki har da jami'in 'yan sanda. Haka nan, bayanai daga yankin sun nuna maharan sun ƙona motoci da kayayyakin aikin da ke harabar ofishin. Jami'in Hulɗa da Jama'a na 'Yan Sandan Jihar, Daniel Ndukwe, ya tabbatar da faruwar lamarin, sai dai babu wani ƙarinbayani da ya yi a kan batun.
Read More
INEC ta yi bayani kan yadda sabon injin rajista ke aiki

INEC ta yi bayani kan yadda sabon injin rajista ke aiki

Daga WAKILINMU Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta bayyana cewa ta yanke shawarar yin aiki da na'urar rajistar masu zaɓe ta zamani ne wajen aikin rajistar masu zaɓe saboda zurfafa aiki da fasahar zamani a tsarin. Babban kwamishina kuma shugaban kwamitin wayar da kan masu zaɓe da yaɗa labarai a INEC, Mista Festus Okoye, shi ne ya bayyana haka a lokacin wata tattaunawa da ya yi da Hukumar Dillancin Labarai ta Nijeriya (NAN) a ranar Litinin a Abuja. Ya bayyana cewa na'urorin, mai suna 'Voter Enrolment Device' (VED), wadda an ƙirƙire ta bisa tsarin 'android' na ƙaramar komfuta ta 'tablet',…
Read More