2023: Duk jam’iyyar da ta tsayar da ɗan Arewa za ta faɗi zaɓe – Akeredolu

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja

Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Kudu kuma Gwamnan Jihar Ondo, Mista Oluwarotimi Akeredolu, a ranar Talata, ya yi gargaɗin cewa, duk jam’iyyar da ta kuskura ta sanya ɗan Arewa a matsayin ɗan takarar Shugaban Ƙasa a shekarar 2023, to za ta faɗi ƙasa warwas.

Gwamna Akeredolu ya bayyana cewar gwamnoni a yankin Arewa na ƙasar dake ƙarƙashin inuwar Ƙungiyar Gwamnonin Kudu a shirye take domin tabbatar da cewa shugaban ƙasa ya fito daga yankin Kudu.

Gwamnan ya bayyana haka a ofishin sa a lokacin da ‘ya’yan jam’iyyar suka kawo masa ziyara masu rajin maida mulki a yankin Kudu ƙarƙashin jagorancin shugaban ƙungiyar Dr. Pogu Bitrus.

Gwamnan wanda suke sukar tsarin karɓa-karɓa suna kawo matsala a kasancewar Nijeriya, domin ya yi imani a adalci.