AFCON 2022: Super Eagles ta tsallake siraɗi


Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa ta Nijeriya, Super Eagles, ta samu nasarar shiga gasar Cin Ƙofin Ƙasashen Afirka (AFCON) wadda aka shirya gudanarwa a ƙasar Kamaru a 2022.

Nijeriya ta samu wannan nasarar ce sakamakon kunnen doki na rashin jefa ƙwallo a raga da Lesotho da Saliyo suka yi a rana ta biyar na buga wasan cancantar shiga gasar.