Amurka ta haramta wa wasu ‘yan Nijeriya biza kan yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasa

Gwamnatin Amurka ta ce ta ɗauki matakan haramta wa wasu ‘yan Nijeriya bizar shiga ƙasar saboda yi wa tsarin dimokuraɗiyya zagon ƙasa a lokacin zaɓuɓɓukan 2023 a ƙasar.

Bayanin haka na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da Sakataren Harkokin Wajen Amurka, Anthony Blinken, ya fitar a ranar Litinin, 15 ga Mayu, 2023, wadda aka wallafa a shafin intanet na gwamnatin Amurka.

A cewar Sakataren “A yau, ina sanar da cewa mun ɗauki matakan ƙaƙaba takunkumin biza ga wasu ‘yan Nijeriya saboda aikata zagon ƙasa ga tsarin dimokradiyya a lokacin zaɓukan Nijeriya na 2023.”

Blinken ya ƙara da cewa, “Amurka ta ƙuduri aniyar tallafawa da kuma ciyar da dimokuraɗiyya gaba a Nijeriya da ma duniya baki ɗaya.”

Haka nan, ya ce takunkumin bizar ya keɓanta ne da wasu mutane amma ba a kan al’ummar Nijeriya ko gwamnatin ƙasar ba.