An kammala musabaƙar Ƙur’ani karo na 35 a Jos

Daga UMAR M. GOMBE

A Lahadin da ta gabata aka kammala musabaƙar karatun Alƙur’ani karo na 35 a garin Jos, Jihar Filato, ƙarƙashin Ƙungiyar Jama’atu Nasril Islam (JNI).

Da yake jawabi a wajen taron, Babban Sakataren JNI, Sheikh Khalid Aliyu Abubakar, ya yi kira ga iyaye da su kula da tarbiyyar ‘ya’yansu da kuma ba su ilimi mai inganci domin samun zaman lafiya da tsaron da ake fata a ƙasa baki ɗaya.

Ya ce, “Wajibi ne a kan iyaye su tabbatar
da sun bai wa ‘ya’yansu nagartacciyar tarbiyya tare da ilimantar da su.”

Yana mai cewa, “sha’anin tsaro shi ne ƙashin bayan kowace al’umma wanda cigaban ƙasa ba ya samuwa sai da tsaro.”

Daga nan, Sheikh Aliyu ya buƙaci ‘yan Nijeriya su kasance masu yi wa ƙasa addu’a domin samun daidaito.