An sako ɗaliban Sakandaren Kagara

Daga FATUHU MUSTAPHA

Bayanai daga Jihar Neja sun nuna an sako ɗalibai da malamai na Sakandaren Kimiyya Kagara da ‘yan bindiga suka yi garkuwa da su ‘yan kwanakin da suka gabata.

Wata majiya mai tushe ta tabbatar wa jaridar PRNigeria batun sakin ɗaliban a safiyar wannan Asabar.

Idan dai za a iya tunawa, Manhaja ta ruwaito batun sace ɗaliban su 27 da ma’aikata 3 da iyalansu su 12, a ranar 17 ga Fabrairun 202.