12
Dec
Daga ABBA MUHAMMAD a Kaduna Sakamakon samun wasu daga cikin manyan ma'aikatan gwamnatin Jihar Kaduna da kuma mutum biyar daga cikin iyalin sa da kamuwa da cutar korona, Gwamna Nasiru Ahmad El-Rufa'i ya sake killace kan sa har sa har sai an yi masa gwaji. Gwamnan ya bayyana haka ne a daren Juma'a a cikin wani bidiyo mai tsawon minti 1:15. Wannan shi ne karo na biyu da ya killace kan sa bayan tabbatar da ci-gaba da hauhawar kamuwa da cutar a Jihar Kaduna da sauran jihohin Nijeriya. A bidiyon, gwamnan ya ce, "Ana ta ci gaba da kamuwa da…