Kimanin sa’o’i 48 da sukar matakin haramta Tiwita da Gwamnatin Tarayyar Nijeriya ta ɗauka, gwamnatin ta gayyaci wakilan ƙasashen Amurka da Birtaniya da Kanada a Nijeriya da su bayyana a gabanta.
Sanarwar gayyatar ta fito ne ta hannun Kimiebi Ebienfa na sashen Sanya Ido Kan Suka da Sadarwa na Ma’aikatar Harkokin Waje ta Nijeriya.
A cewar jami’in, “Biyo bayan haramta Tiwita da Gwamnatin Tarayya ta yi da kuma bayanan da wasu jakadu a Nijeriya suka yi a kan batun dakatarwar, an buƙaci in sanar cewa Ministan Harkokin Waje, Geoffrey Onyeama ya gayyaci jakadun da lamarin ya shafa zuwa wajen taro da tsakar ranar wannan Litinin a babban zauren taron ma’aikatar.”
Haka nan, gayyatar ta buƙaci halartar ‘yan jarida domin shaida abin da taron zai tattauna.