Bayan shekara 28, Buhari ya cika alƙawarin bai wa ‘yan wasan Super Eagles gidaje

Daga WAKILINMU

Shekaru 28 bayan da Gwamnatin Tarayya ta yi wa ‘yan wasan Super Eagles alƙawarin gidaje kyauta, sai a wannan karon Shugaba Muhammadu Buhari ya cika wannan alƙawari da gwamnatocin baya suka kasa cikawa.

Bayanin hakan ya fito ne daga bakin Shugaba Buhari da kansa a lokacin da ya ke ƙaddamar da sababbin gidaje da gwamnatinsa ta gina a Lafiya, Babban Birnin Jihar Nasarawa a ƙarshen makon jiya, yana mai cewa, gwamnatinsa a shirye ta ke wajen saka wa duk ɗan ƙasar da ya yi aiki tuƙuru wajen gina Nijeriya.

Idan dai za a iya tunawa, a 1994 Gwamnatin Nijeriya ta yi wa ‘yan wasan da suka lashe Gasar Kofin Afrika da aka gudanar a Ƙasar Tunisiya, inda cika wannan alƙawari a yanzu ya gwada yadda Gwamnatin Shugaba Buhari ke ƙoƙarin dawo da karsashin ‘yan wasan Nijeriya a kowane mataki.