Bidiyo: Yadda iyayen yaran da aka sace a Kaduna suka muzanta kwamishina

Iyayen yaran da ‘yan bindiga suka sace a Makarantar Bethel Baptist High a Kaduna a Litinin da ta gabata, sun nuna wa Kwamishinan Tsaro na Cikin Gida na Jihar, Samuel Aruwan, ɓacin ransu inda suka yi masa ihu suka kore shi a lokacin da shi da tawagarsa suka ziyarce su a harabar makarantar da lamarin ya faru.