Buhari ya cancanci yabo bisa magance rikicin manoma da makiyaya – Garba Shehu

Daga MAHDI M. MUHAMMAD

Babban mataimaki na musamman ga shugaban ƙasa Muhammad Buhari kan harkokin yaɗa labarai, Malam Garba Shehu, ya bayyana cewa, shugaban ya cancanci yabo bisa ƙoƙarin da ya yi na magance rikicin manoma da makiyaya a ƙasar nan.

Shehu ya bayyana hakan ne a jiya Juma’a a lokacin da yake gabatar da wata takarda mai taken ‘Labaran ƙarya: ƙalubalen sarrafa bayanai’ a wajen bikin cika shekara 10 da kafa Jami’ar Tarayya ta Dutsin-Ma (FUDMA), da ke jihar Katsina.

Ya ƙara da cewa, “tabbas gwamnatin Buhari ce kawai gwamnatin Nijeriya da ta samar da hanyar da za ta bi wajen magance ƙalubalen makiyaya da manoma a duk tsawon shekarun da aka samu ’yancin kai.”

“Barazanar da jama’a ke yi da zaman lafiya tsakanin ƙabilu da addinai daban-daban daga rikicin manoma, rikicin makiyaya, ’yan fashi da rikicin filaye, abin damuwa ne sosai ga gwamnatin Buhari. Ba daidai ba ne a riƙa cewa gwamnati na da ko ba ta yin wani abu don magance barazanar. Na farko dai ana ci gaba da ƙoƙarin kafa wuraren kiwo don hana ko daƙile kiwo a bayyane, abin ada ke kawo rikici tsakanin makiyaya da manoma,” inji shi.

Ya ce, “wannan tsohuwar matsala ce da ke fuskantar gwamnatocin Nijeriya tun zamanin mulkin mallaka. Duk da haka, ana magance batutuwan rabon filaye a matakin jiha. Wannan yana nufin dole ne gwamnonin jihohi su nuna goyon baya don ciyar da tsarin gaba. Gwamnatin tarayya ta ƙaddamar da wani shiri a shekarar da ta gabata domin haɗa hannu da jihohi domin magance waɗannan matsaloli tare.”

Ya ci gaba da cewa, “abin takaici shi ne, an yi rashin hakan a wasu jihohin da kuma batun dogon yaƙin da ake yi da Boko Haram; ‘Yan Nijeriya sun san irin ƙoƙarin da wannan gwamnati ta yi. Lokacin da gwamnati ta hau kan karagar mulki, ƙungiyar ta’addanci ta riƙe tare da gudanar da wani yanki mai girman ƙasar Belgium. Yanzu ba su riƙe ko ɗaya ba. ‘Yan ta’addan suna fakewa ne a cikin dazuka masu nisa da kuma kan iyakoki.”

“Wannan ya sa da wuya a kashe wutar ta ƙarshe ta tayar da (ayar baya, kuma gwamnati ba ta da tunanin irin barazanar da ake fuskanta. Alƙaluma na baya-bayan nan sun nuna cewa sama da ‘yan Boko Haram 14,500 ne suka miƙa wuya bisa raɗin kansu. Sannan kuma, ba za a iya hana ci gaban da aka samu ba. Dangane da ƙaruwar laifuka da rashin tsaro, an ƙaddamar da sabon shirin gwamnati na aikin ’yan sanda,” inji shi.

Ya ƙara da cewa, “an ɗauki sabbin jami’an ‘yan sanda 10,000 kuma ana shirin ɗaukar wasu 10,000 daga yankunan da za su kiyaye saɓanin yadda ake yi a baya. Gwamnati na fatan hakan zai kawo kusantar ‘yan sanda ga al’ummomin yankin. An ware Naira biliyan 13 don shirin farko. Bisa tsarin, duk shekara za a ga ƙarin ‘yan sanda 10,000. Ra’ayi ne cewa kalaman shugaban kan IPOB, wanda ya kai ga dakatar da manhajar tuwita a Nijeriya wanda ke sanya cece-kuce. Ga mutane da yawa hakan bai kasance ba.”

Tun da farko, a jawabinsa na maraba, mataimakin shugaban jami’ar Farfesa Armaya’u Hamisu Bichi, ya ce, abin farin ciki ne sosai ganin an shafe shekaru goma da kafa cibiyar.

“Ba abu ne mai sauƙi ba a bunƙasa cibiya tun daga farko zuwa matakin da ta ke a yanzu. Ita ce mafi kyau a cikin sauran jami’o’in FUDMA da aka kafa tare,” inji shi.