Labarai

Ina goyon bayan sauye-sauyen da Gwamna Raɗɗa ke yi a Jihar Katsina – Masari

Ina goyon bayan sauye-sauyen da Gwamna Raɗɗa ke yi a Jihar Katsina – Masari

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Tsohon Gwamnan Jihar Katsina, Alhaji Aminu Bello Masari ya bayyana ra'ayinsa akan salon kamun ludayin Gwamnan jihar, Malam Dikko Umar Raɗɗa. Masari ya bayyana ra'ayin na sa ne da yake jawabi a wurin wani taron liyafar cin abincin dare da Dattawan Jam'iyyar APC na jihar Katsina suka shirya domin karrama shi tare da yin addu'o'in samun nasara ga sabon Gwamnan da ta gudana a ɗakin taro na Paramount dake cikin birnin Katsina. A cewar Gwamna Masari, yana tare da Dikko Raɗɗa ɗari bisa ɗari kuma yana goyon bayan sauye-sauyen da yake yi domin inganta…
Read More
An yi kira ga sabbin jami’an hana fasa ƙwauri 335 da aka yaye a Kano su zama jakadu nagari

An yi kira ga sabbin jami’an hana fasa ƙwauri 335 da aka yaye a Kano su zama jakadu nagari

Daga IBRAHIM MUHAMMAD a Kano Kwalejin Horas da Jami'an Hana Fasa Ƙwauri ta Ƙasa dake Gordon dutse a jihar Kano ta yaye sabbin jami'ai da suka kammala karvar horo guda 335. Taron wanda ya samu baquncin mataimakin kwanturola na qasa mai kula da sashin bincike, Muhammad Abba Kurra. Da yake jawabi mataimakin kwanturola janar na hukumar ya ce waɗanda aka yaye ɗin su zama jakadun hukumar a duk inda za a kaisu, aikinsu nagari zai ƙarawa hukumar daraja akasin haka kuma zai zubar musu da kima. Ya yi kira gare su akan su yi aiki da doka da ƙa'ida ta…
Read More
Sabbin Hafsoshin Soja: Janar-Janar 103 na fuskantar ritaya

Sabbin Hafsoshin Soja: Janar-Janar 103 na fuskantar ritaya

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Baya ga shirin ritayar da ake shirin yi, za a kara wa jami’ai da dama ƙarin girma zuwa matsayi na gaba don cike guraben da manyan hafsoshin da suka yi ritaya za su samar a wani vangare na sake tsara ayyukan da sabbin shugabannin ma’aikata ke yi. Hakan dai na faruwa ne watanni shida bayan da manyan hafsoshin soja 24 da birgediya-janar 38 suka yi ritaya a watan Disambar da ta gabata bayan shafe shekaru 35 suna hidimar ƙasar. Tinubu ya sanar da murabus ɗin Janar Lucky Irabor wanda shi ne babban hafsan tsaron…
Read More
N3m kacal na tarar a asusun Zamfara – Gwamna Dauda

N3m kacal na tarar a asusun Zamfara – Gwamna Dauda

'Da bashi nake gudanr da harkokin jihar' Daga BASHIR ISAH Gwamnan Jihar Zamfara,Dauda Lawal Dare, ya bayyana cewa, Naira miliyan uku kacal ya tarar a asusun jihar bayan da ya karɓi mulki ranar 29 ga mayu. Gwamna Lawal ya bayyana haka ne a hirar da BBC Hausa ta yi da shi a ranar Litinin. Lawal ya ce gwamnatin da ya gada ta gaza biyan albashin ma'aikata na wata uku a jere kafin mulki ya dawo hannunsa. “Mummunan yanayi muka gada,” in ji Lawal. Ya ci gaba da cewa, “Gwamnatin da ta gabata ta bar asusun jihar a bushe babu komai.…
Read More
Rusau a Kano: Ƙungiya ta yi barazanar maka Gwamna Abba a kotu

Rusau a Kano: Ƙungiya ta yi barazanar maka Gwamna Abba a kotu

Ta bai wa Gwamnan sa'o'i 72 ya janye aikin rusau da yake yi Daga BASHIR ISAH Ƙungiyar Good Governance and Change Initiative (GGCI), ta bai wa Gwamnan Jihar Kano, Abba Yusuf, wa'adin sa'o'i 72 a kan ya dakatar da rusau da yake yi a jihar sannan ya gayyato 'yan kasuwa da ɗaiɗaikun mutanen da lamarin ya shafa don warware matsalar cikin ruwan sanyi. Ƙungiyar ta yi barazanar maka Gwamnan a kotu muddin wa'adin da ta shata masa ya ƙare ba tare da yin abin da ya kamace shi ba. Yayin da yake yi wa manema labarai jawabi a ranar Talata…
Read More
Gwamnan Kano ya miƙa sunayen kwamishinoni ga majalisar jihar

Gwamnan Kano ya miƙa sunayen kwamishinoni ga majalisar jihar

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya miƙa sunayen mutane 19 da yake son ya naɗa a matsayin kwamishinoni a majalisar zartarwar jihar. A ranar Talata ce Shugaban Majalisar Dokokin Jihar, Honorabul Yusuf Falgore, ya karanto jerin sunayen da gwamnan ya aike wa majalisar. Waɗanda aka zaɓa ɗin dai za su hallara gobe Laraba da ƙarfe 10:00 na safe a gaban majalisar dokokin domin tantancewa. Ga jerin sunayen kamar haka: Comrade Aminu Abdulsalam Hon. Umar Doguwa Ali Haruna Makoda Hon. Abubakar Labaran Yusuf Hon. Danjuma Mahmoud Hon. Musa Shanono Hon. Abbas Sani Abbas Haj. Aisha…
Read More
Gwamnan Kaduna ya bai wa tsohon ma’aikacin Jaridar Blueprint muƙami

Gwamnan Kaduna ya bai wa tsohon ma’aikacin Jaridar Blueprint muƙami

Daga BASHIR ISAH Gwamna Uba Sani na Jihar Kaduna ya naɗa tsohon ma'aikacin Jaridar Blueprint, Samuel Aruwan, a matsayin Shugaban Hukumar Kula da Birnin Kaduna (KCTA). Aruwan, wanda ya kasance Kwamishinan Tsaro da Harkokin Cikin Gida na jihar Kaduna a baya-bayan nan, tsohon wakilin Jaridar Blueprint ne a jihar kafin daga bisani ya zama shugaban ofishin jaridar na Kaduna. Masanin aikin jarida ne wanda ke da ƙwarewar aiki na shekaru da dama inda a shekarar 2015 ya koma aiki da gwamnati. Sanarwar da Sakataren Yaɗa Labarai ga Gwamnan, Muhammad Lawal Shehu, ya fitar a ranar Talata yaba da ƙwarewar Aruwan…
Read More
An rantsar da sabbin alƙalan Kotun Ma’aikata shida

An rantsar da sabbin alƙalan Kotun Ma’aikata shida

Daga NASHIR ISAH A wani mataki na ƙarfafa ɓangaren shari'a na ƙasa, Alƙalin-alƙalai na Nijeriya (CJN), Mai Shari'a Olukayode Ariwoola, ya rantsar da wasu alƙalai sabbin ɗauka su shida na Kotun Ma'aikata. Rantsarwar ta gudana ne a Kotun Ƙolin da ke Abuja a ranar Litinin. Yayin rantsarwar, Mai Shari'a Ariwoola ya yi kira ga sabbin alƙalan da su yi aikin da ya rataya a kansu bilhaƙƙi da kuma martabawa daidai da tanadin dokar ƙasa. Ya ƙara da cewa, ɓangaren shari'ar ƙasar nan na buƙatar maza da mata masu nagarta waɗanda za su kwatanta gaskiya ga 'yan ƙasa ba tare da…
Read More
Tsohon Gwamnan Binuwai, Samuel Ottom ya amsa gayyatar EFCC

Tsohon Gwamnan Binuwai, Samuel Ottom ya amsa gayyatar EFCC

Tsohon Gwamnan Jihar Binuwai, Samuel Ortom, ya amsa gayyatar Hukumar Yaƙi da yi wa Tattalin Arziki Ta'annati (EFCC). A ranar Talata EFCC ta gayyaci tsohon gwamnan don amsa mata tambayoyi kan abin da ya shafi zamanin mulkinsa. Majiyarmu ta ce Ortom ya isa harabar ofishin hukumar da ke Makurdi ne da misalin ƙarfe 10:08 na safe. Ƙarin bayani na tafe...
Read More
Tinubu zai yi ziyarar aiki ta farko tun bayan kama mulki

Tinubu zai yi ziyarar aiki ta farko tun bayan kama mulki

Daga BASHIR ISAH Shugaba Bola Ahmed Tinubu zai tafi ziyarar aiki Paris, babban birnin ƙasar Faransa ya zuwa ranar Alhamis, 22 ga Yuni. Wannan ita ce ziyara ta farko da Tinubu zai yi a matsayin Shugaban Ƙasa. Tinubu zai yi ziyarar ce domin halartar taron shugabannin duniya inda za su rattaɓa hannu kan Sabuwar Dokar Kuɗi ta Duniya wadda za ta da ba da fifiko kan ƙasashe marasa ƙarfi wajen samun tallafi da zuba jari biyo bayan matsanancin sauyin yanayi da kuma bayan tasirin annobar Korona. Taron wanda na yini biyu ne, zai gudana ne daga ranar 22 zuwa 23…
Read More