07
Feb
Daga AISHA ASAS Wasu 'yan bindiga sun kai hari a Tungan Maje da ke yankin Gwagwalada, Abuja, inda suka yi garkuwa da wasu mutum huɗu. Al'amarin wanda ya auku a tsakar daren wannan Lahadin, sai da 'yan bindigar suka shafe kimanin sa'o'i uku suna abin da suka ga dama a Tungan Maje kafin daga bisani suka yi awon gaba da wani tsohon jami'in Hukumar Kula da Shige da Fice ta Nijeriya (NIS) Abdulahi Idris Rakieu da wasu mutum biyu daga iyalan gidansa. A cewar jaridar TheCable, harin ya shafi wani mai suna Olusola Agun, wanda shi ya zama cikon na…