Labarai

Alhaji MK Ahmed ya kwanta dama

Alhaji MK Ahmed ya kwanta dama

Daga WAKILINMU Allah Ya yi wa Sarkin Yaƙin Lokoja, Alhaji MK Ahmed (MFR), rasuwa. Marigayin wanda tsohon sakatare ne ga marigayi Malam Aminu Kano, ya rasu ne da safiyar Asabar bayan fama da rashin lafiya. Jaridar Prime Time ta rawaito cewa, marigayin ya bar duniya yana da shekara 89. Ya rasu ya bar 'ya'ya da dama, ciki har da Barista Naseer Ahmed, mamallakin fitaccen Otale ɗin Grand Central da ke Kano.
Read More
INEC za ta yi kaka-gida a rumfunan zaɓe don hana sayen ƙuri’u

INEC za ta yi kaka-gida a rumfunan zaɓe don hana sayen ƙuri’u

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Gabanin zaɓen shekarar 2023, Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) ta ce, za ta magance matsalolin da suka sava wa doka kan kuɗaɗen yaƙin neman zaɓe da kuma abin da ta kira ‘al’adar sayen kuri’u’ a rumfunan zaɓe a ranar zaɓe’. Don haka, hukumar ta ce, a jiya Alhamis, 24 ga Nuwamba, 2022 ne ta fitar da taƙaitaccen bayani kan ƙa’idojin kuɗi da kuɗaɗen zaven jam’iyyu da ’yan takara. Shugaban hukumar ta INEC, Farfesa Mahmood Yakubu, ya bayyana haka a ranar Laraba a wani taron masu ruwa da tsaki da ƙungiyar 'Civil Society Situation…
Read More
Gaskiyar yadda Sajan Rogers ya kashe mahaifiyarmu, inji ’ya’yan Kudirat Abiola

Gaskiyar yadda Sajan Rogers ya kashe mahaifiyarmu, inji ’ya’yan Kudirat Abiola

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Sama da shekaru 26 bayan kisan gillar da aka yi mata, ’ya’yan marigayiya Kudirat Abiola, wadda ta lashe zaɓen shugaban ƙasa da aka soke ranar 12 ga watan Yunin 1993, sun tuhumi Manjo Hamza Al Mustapha, tsohon babban jami’in tsaro (CSO) ga Marigayi Janar Sani Abacha da kitsa kashe mahaifiyarsu. ’Ya’yan marigayiya Kudirat Abiola sun ƙalubalanci Manjo Hamza Al Mustapha su na masu ikirarin cewa mataimakin shugaban ƙasa Yemi Osinbajo ne ya ingiza Sajan Rogers ya sanya sunansa a matsayin wanda ya kashe mahaifiyarsu. Yaran Kudirat a wata sanarwa da suka fitar kuma suka sanyawa hannu…
Read More
Kotu ta yi wa Faisal Maina sassaucin zaman gidan yari

Kotu ta yi wa Faisal Maina sassaucin zaman gidan yari

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Kotun Ɗaukaka Ƙara mai zamanta a Abuja ta tabbatar da hukuncin ɗaure Faisal, ɗan tsohon Shugaban Hukumar Fansho da aka rusa, Abdulrasheed Maina bisa laifin haɗa baki da sace kuɗin ƙasa. A hukuncin da kotun ta yanke a jiya Alhamis, alƙalai uku da suka yi zama sun rage wa'adin da aka ɗiba masa na shekaru 14 zuwa bakwai tun da wannan laifinsa ne na farko.  Mai shari'a Ugochukwu Anthony Ogakwu da ya jagoranci hukuncin ya bayyana cewa, mai Shari'a Okon Abang na Kotun Tarayya da ke Abuja ya yi gaskiya wajen ɗaure Faisal. Sai…
Read More
Ƙasar Nijar ta saka sunan Shugaba Buhari a wata hanya

Ƙasar Nijar ta saka sunan Shugaba Buhari a wata hanya

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja A ranar Alhamis ne Fadar Shugaban Ƙasa ta bayyana cewa Jamhuriyar Nijar ta sanya sunan Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari a wata hanya a ƙasar, wanda a cewar sanarwar alama ce da ke nuna irin mutuntawar da makwafciyar ƙasar ta Nijeriya ke yi masa. Babban mai taimaka wa shugaban ƙasa na musamman kan harkokin yaɗa labarai da wayar da kan jama’a, Malam Garba Shehu ne ya bayyana hakan a Yamai, babban birnin ƙasar Nijar, jim kaɗan bayan da Mista Buhari ya ƙaddamar da wata babbar hanya mai sunan sa. Garba Shehu ya ce Shugaban Jamhuriyar…
Read More
Ambaliyar ruwa: Ɗantata, Abdussamad da sauran al’umma sun haɗa tallafin Naira biliyan ɗaya a Jigawa

Ambaliyar ruwa: Ɗantata, Abdussamad da sauran al’umma sun haɗa tallafin Naira biliyan ɗaya a Jigawa

Daga UMAR AKILU MAJERI a Dutse Hamshaƙan 'yan kasuwa kuma masu taimako, Alhaji Aminu Ɗantata da Abdulsamad Isyaku Rabi’u, mamallakin kamfanin BUA Group, sun haɗa tallafin sama da Naira biliyan ɗaya ga waɗanda ambaliyar ruwa ta shafa a Jihar Jigawa. An bada tallafin ne a taron haɗa tallafi ga waɗanda ambaliyar ruwa ta ɗaiɗaita a ranar Asabar a birnin Dutse na Jihar Jigawa. Ɗantata da Abdulsamad kowannen su ya bada gudunmawar Naira miliyan 200, inda gwamnatin Jigawa ta bada Naira miliyan 250, sai kuma Gwamnan Jihar, Muhammad Badaru, ya bada gudunmawar Naira miliyan 25. Ɗantata, wanda ya samu wakilcin Alhaji…
Read More
Nijeriya za ta faɗa cikin matsalar abinci a 2023, inji IMF

Nijeriya za ta faɗa cikin matsalar abinci a 2023, inji IMF

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Asusun Lamuni na Duniya IMF, ya ce Nijeriya na fuskantar barazanar faɗawa cikin matsalar abinci a 2023, saboda hauhawar farashi da kuma ambaliyar ruwa da ta ɗaiɗaita amfani gona da tsadar taki. A cewar ƙiddidigar hukumar NBS, hauhawar farashi a Nijeriya ya kai maki 23.72 cikin 100 a watan Oktoban 2022, yayin da farashin wasu kayayyakin abinci ya ƙaru daga kashi 50 zuwa 100. IMF ta ce la'akari da wannan yanayi da ake ciki, farashin kayan abinci zai munana a 2023. Sannan rahoton IMF ya ce duk da irin waɗannan matsaloli, akwai kuma yaƙin…
Read More
Ilimin ‘ya’ya mata: Bankin Duniya ya sake tallafa wa Nijeriya da miliyan $700

Ilimin ‘ya’ya mata: Bankin Duniya ya sake tallafa wa Nijeriya da miliyan $700

Daga BASHIR ISAH Bankin Duniya ya jadda aniyarsa na tallafa wa ilimin 'ya'ya mata a Nijeriya inda ya sake ware Dala miliyan $700 a matsayin gudunmawarsa ga fannin ilimin na 'ya'ya mata a ƙasar. Dala miliyan $700 ɗin ƙari ne a kan abin da Bankin ya bayar a baya. Bankin ya ce, ya ba da tallafin ne domin bai wa 'ya'ya mata marasa galihu damar kammala karatun sakandare. A baya Bankin ya ba da tallafin Dala miliyan $500 don tallafa wa karatun 'ya'ya mata a wasu jihohi 7 na ƙasar. A cewar Bankin tallafin baya-bayan zai shafi wasu jihohin ƙasar…
Read More
Buhari ya ƙaddamar da sabbin takardun N200, N500 da N1000

Buhari ya ƙaddamar da sabbin takardun N200, N500 da N1000

Daga WAKILINMU A ranar Laraba Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya ƙaddamar da sabbin takardun Naira 200 da 500 da kuma 1000 bayan sake musu fasali. Buhari ya ƙaddamar da sabbin takardun Naira ɗin ne a wajen taron Majalisar Zartarwa a Abuja. Idan za a iya tunawa, ranar 26 ga Oktoba n 2022, Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya ba da sanarwar shirin Gwamnatin na neman sake fasalin takardun kuɗin da lamarin ya shafa. Tare da cewa, an ɗauki matakin hakan ne domin kula da kuɗaɗen da ke hannun 'yan ƙasa ana hada-hada da su. CBN ya ce tsaffin takardun Naira da…
Read More
Buhari zai ƙaddamar da sabbin takardun Naira ran Laraba

Buhari zai ƙaddamar da sabbin takardun Naira ran Laraba

Daga BASHIR ISAH A wannan Larabar ake sa ran Shugaban Ƙasa, Muhammadu Buhari zai ƙaddamar da sabbin takardun Naira da aka sauya wa fasali. Takardun Naira da aka sake wa fasalin sun haɗa da N1,000 da N500 da kuma N200. Shugaban Babban Bankin Nijeriya (CBN), Godwin Emefiele ne ya bayyana haka ranar Talata a wajen taron da bankin ya saba gudanarwa duk wata a Abuja. Shugaban CBN ya ce ba za a ƙara wa'adin da aka tsayar ba tun farko don mayar da tsofoffin tarkadun Naira da sauyin ya shafa zuwa banki. A ranar 26 ga Oktoba Emefiele ya ba…
Read More