Labarai

Gwamnatin Tarayya ta fara karɓe kadarorin waɗanda ke ɗaukar nauyin ta’addanci a Nijeriya

Gwamnatin Tarayya ta fara karɓe kadarorin waɗanda ke ɗaukar nauyin ta’addanci a Nijeriya

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja A cigaba da daƙile ayyukan ta'addanci da ake fuskanta a lungu da saƙon ƙasar nan, Gwamnatin Nijeriya ta fara ƙoƙarin karɓe kadarorin waɗanda aka gano suna taimaka wa ko ɗaukar nauyin 'yan ta'adda ta hanyar amfani da kuɗaɗensu da shawarwarin su da dai sauransu don haɓaka ta'addanci a cikin ƙasar. Kamar yadda wasu gidajen jaridu suka rawaito, sun ce jami'an tsaro da sauran hukumomin ƙwararru a kan lamuran tsaro suna bibiyar kadarorin masu taimaka wa 'yan ta'adda da suka haɗa da kamfanoni da asusun ajiya na banki da kuma wasu ƙungiyoyi masu alaƙa da…
Read More
Sojoji sun hallaka mai kai wa su Turji makamai a Shinkafi

Sojoji sun hallaka mai kai wa su Turji makamai a Shinkafi

Daga BASHIR ISAH A wani samame da Rundunar Mayaƙan Sama ta Nijeriya (NAF) ta kai da jirigin yaƙinta a Jihar Zamfara, Rundunar ta samu nasarar kashe Malam Ila wanda ya yi ƙaurin suna waje safarar makamai a ƙauyen Manawa cikin Ƙaramar Hukumar Shinkafi a jihar. Majiyar PRNigeria ta ce, Ila shi ne babban mai yi wa ‘yan ta’adda safarar makamai, musamman ma Bello Turji a Zamfara. Majiyar ta ce, “A ranar 18 ga Nuwamban 2022 NAF a ƙarƙashin Operation Hadarin Daji suka kai samamen inda aka hallaka Malam Ila. “Malam Ila ya kasance wanda ake nema ruwa a jallo saboda…
Read More
Jami’ar Jihar Kwara ta yi babban rashi

Jami’ar Jihar Kwara ta yi babban rashi

Daga BASHIR ISAH Allah Ya yi Mataimakin Shugaban Jami'ar Jihar Kwara (KWASU), Muhammed Akanbi, rasuwa. Marigayin wanda farfesa ne a fannin doka kuma Babban Lauyan Nijeriya (SAN), ya bar duniya yana da shekara 51. Rijistaran jami'ar ya tabbatar da rasuwar marigayin cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi da daddare. “Cikin alhini da sadaukarwa ga Allah, Hukumar Gudanarwar ta Jami'ar Jihar ke sanar da rasuwar Mataimakin Shugaban jami'ar, Farfesa Muhammed Mustapha Akanbi SAN,” inji sanarwar. An naɗa marigayi Akanbi a matsayin Mataimakin Shugaban KWASU ne a watan Afrilun 2020. Marigayin ɗa ne ga shugaban hukumar ICPC na farko, marigayi…
Read More
Bayan tilasta biyan ‘Kuɗin Kariya’, ’yan bindiga sun wawushe mutum 44 a ƙauyen Zamfara

Bayan tilasta biyan ‘Kuɗin Kariya’, ’yan bindiga sun wawushe mutum 44 a ƙauyen Zamfara

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Aƙalla mutum 44 ne ’yan bindiga suka yi awon gaba da su a ƙauyen Kanwa da ke Ƙaramar Hukumar Zurmi ta Jihar Zamfara. Mazauna yankin sun ce maharan sun yi wa ƙauyen ƙawanya ne cikin dare, inda suka riƙa bi gida-gida suna kwasar mutane, galibi mata da ƙananan yara. A baya-bayan nan dai, an ɗan sami salamar yawan satar mutane a ƙauyukan Zamfara, amma bisa ga dukkan alamu a ’yan kwanakin nan, cikin mazauna ƙauyukan ya fara ɗurar ruwa saboda yadda lamarin ya sake dawowa. Ana dai zargin cewa riƙaƙƙen ɗan bindigar nan na yankin, Dankarami…
Read More
‘Yan bindiga sun yi garkuwa da mutum 20 a Zamfara

‘Yan bindiga sun yi garkuwa da mutum 20 a Zamfara

Daga SANUSI MUHAMMAD a Gusau 'Yan bindiga a Jihar Zamfara,sun sace mutum 20 ciki har da wasu tagwaye 'yan mwana huɗu da haihuwa. Wannan na zuwa ne jim kaɗan bayan da Kwamishinan Yaɗa Labarai na jihar, Ibrahim Dosara, ya bayyana cewa an inganta tsaro a jihar. Garkuwa da mutanen ta faru a garin Daura cikin Ƙaramar Hukumar Zurmi a jihar. Wani mazaunin garin, Malam Haruna Ahmad Dauran, ya tabbatar wa Blueprint Manhaja aukuwar hakan a tattaunawar da suka yi ranar Lahadi. A cewarsa, ‘yan bindigar sun mamaye garin ne da misalin ƙarfe 8:30 na safiyar Asabar inda suka fara bincike…
Read More
Dogara Yaro ne Sarkin Hausawan Legas – Tinubu

Dogara Yaro ne Sarkin Hausawan Legas – Tinubu

Daga WAKILINMU Ɗan takarar Jam'iyyar APC kuma tsohon Gwamnan Jihar Legas, Sanata Ahmed Bola Tinubu, ya amince da Alhaji Aminu Dogara a matsayin Sarkin Hausawan Jihar Legas, lamarin da ya warware matsalar shugabanci da ta kunno kai kuma ta dabaibaye al'ummar Arewa mazauna Birnin Ikko, wato Legas. Asiwaju Bola Tinubu ya kawo ƙarshen rikicin ne a ranar Juma'a, 18 ga Nuwamba, 2022, bayan da ya amince da rahoton kwamitin da ya kafa ƙarƙashin jagorancin Gwamnan Jihar Kano, Dr. Abdullahi Umar Ganduje, da Alhaji Lawal Abbas Garba a matsayin Sakataren Kwamitin. A yanzu an amince da Alhaji Aminu Dogara Yaro a…
Read More
Buhari ya amince da ƙarin albashi wa ma’aikatan shari’a

Buhari ya amince da ƙarin albashi wa ma’aikatan shari’a

Daga BASHIR ISAH Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari, ya amince tare da ba da umarnin gaggawa game da aiwatar da ƙarin albashi ga ma'aikatan fannin shari'a. Buhari ya bayyana haka ne sa'ilin da yake jawabi a wajen bikin buɗe wani sashe na Makarantar Lauyoyi a Fatakwal. Hadimin Babban Lauyan Ƙasa kan sha'anin yaɗa labarai da hulɗa da jama'a, Dakta Umar Gwandu, shi ne ya bayyana haka. Babban Lauyan Ƙasa kuma Ministan Shari'a, Abubakar Malami, SAN, shi ne ya wakilci Buhari a wajen taron. A cewar jaridar Punch, Buhari ya buƙaci Hukumar Tara Kuɗin Shiga da Rabawa da kuma Ministan Shari'a da…
Read More
Tinubu ya warware rikicin shugabanci da ya dabaibaye ‘yan Arewa mazauna Legas

Tinubu ya warware rikicin shugabanci da ya dabaibaye ‘yan Arewa mazauna Legas

Daga WAKILINMU Ɗan takarar Jam'iyyar APC kuma tsohon Gwamnan Jihar Legas, Sanata Ahmed Bola Tinubu, ya warware matsalar shugabanci da ta kunno kai kuma ta dabaibaye al'ummar Arewa mazauna Birnin Ikko, wato Legas. Asiwaju Bola Tinubu ya kawo ƙarshen rikicin ne a ranar Juma'a, 18 ga Nuwamba, 2022, bayan da ya amince da rahoton kwamitin da ya kafa ƙarƙashin jagorancin Gwamnan Jihar Kano, Dr. Abdullahi Umar Ganduje, da Alhaji Lawal Abbas Garba a matsayin Sakataren Kwamitin. A yanzu an amince da Alhaji Aminu Dogara Yaro a matsayin Sarkin Hausawan Jihar Legas, yayin da Dr. Mohammad Banbado zai cigaba da kasancewa…
Read More
2023: Duk jihar da rikicin siyasa ya tashi laifin gwamnoni ne – Mathew Kukah

2023: Duk jihar da rikicin siyasa ya tashi laifin gwamnoni ne – Mathew Kukah

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Babban Limamin Ɗariƙar Cocin Katolika na Sakkwato, Mathew Kukah, ya yi kira ga ‘yan Nijeriya cewa su ɗora laifin ɓarkewar rikice-rikicen siyasa a kan gwamnonin jihohi. Ya ce akasari duk rikicin siyasar da ya tashi da wanda zai tashi kafin nan da zaɓen 2023, duk gwamnonin jihohi ne musabbabinsu. Kukah ya yi wannan tsokaci a cikin wata hira da gidan talabijin na Arise TV ya yi da shi a ranar Talata. Ya ce wasu gwamnonin jihohi ƙiri-ƙiri su na hana jam’iyyun siyasa yin amfani wuraren taruka mallakar jihohi, lamarin da faston ya ce hakan…
Read More
Gwamna Buni ya tallafa wa marayu 200 da Naira 50,000 kowanne

Gwamna Buni ya tallafa wa marayu 200 da Naira 50,000 kowanne

Daga MUHAMMAD AL-AMEEN, Damaturu Gwamnan Jihar Yobe, Hon. Mai Mala Buni ya umurci Ma’aikatar Ƙirƙiro Hanyoyin Tattalin Arziki da Ayyuka ta bai wa zawarawa 400 tallafin dogaro da kai. Gwamnan ya bayar da wannan umarnin ne a ranar Asabar a lokacin da ya karɓi baƙuncin marayu 200 daga ƙananan hukumomi 17 dake faɗin jihar. Bugu da ƙari kuma, gwamnan ya tallafa wa kowane maraya ɗaya daga cikin adadin marayu 200 da kyautar Naira 50,000, sannan kuma shaidar da cewa sun cancanci kulawar gwamnati da sauran al’umma baki ɗaya. Ya ce ya zama dole a tallafa musu tare da bai wa…
Read More