Labarai

Yadda rokokin sojojin Nijeriya suka hallaka shugabannin ISWAP, Ali Kwaya da Bukar Mainoka a Chadi

Yadda rokokin sojojin Nijeriya suka hallaka shugabannin ISWAP, Ali Kwaya da Bukar Mainoka a Chadi

Daga AMINA YUSUF ALI Wasu ƙasurguman shugabannin mayaƙan ISWAP, Mallam Ali Kwaya da Mallam Bukar Mainoka, sun haɗu da ajalinsu a hannun jami'an sojin Nijeriya a tafkin Chadi, ranar Asabar ɗin da ta gabata. Dubun Kwaya da Mainoka, waɗanda kuma manya ne a majalisar Shura ta ISWAP ta cika ne a lokacin da tawagar sojin sama ta 'Operation Hadin Kai' ta kai musu samame a garin Belowa. Mamatan biyu suna daga cikin ƙalilan ɗin mayaƙan ISWAP/Boko Haram da suka yi saura a boye a yankin Tumbuns, dake tafkin Chadi a ƙaramar hukumar Abadam. Majiyarmu ta bayyana cewa, Sojojin Nijeriya sun…
Read More
Gwamnatin Kano za ta maka Sahara Reporters a kotu idan ba ta janye rahotonta, ta ba Ganduje haƙuri ba – Kwamishina

Gwamnatin Kano za ta maka Sahara Reporters a kotu idan ba ta janye rahotonta, ta ba Ganduje haƙuri ba – Kwamishina

Daga AMINA YUSUF ALI Gwamnatin jihar Kano ta nemi jaridar Sahara Reporters (SR) da ta ba ta haƙuri kuma sannan ta janye rahotonta a kan Ganduje. Bayan sakamakon rahoton EFCC ya wanke gwamnan jihar Kano Dakta Abdullahi Umar Ganduje a kan rahoton da jaridar ta wallafa cewar yana daga gwamnonin Nijeriya waɗanda EFCC ta kasafta a jerin waɗanda suke voye Naira a gidajensu. Hakazalika, gwamnatin jihar Kano ta yi zazzafan Allah wadai ga wani rahoto da jaridar yanar gizon mai suna SR, cewar Gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje yana cikin jerin gwamnoni guda uku da suke ɓoye Nairori a…
Read More
Sojojin ruwa sun fara aikin hizba a Fatakwal, sun afka wa gidan karuwai, sun tserar da ‘yan mata 50

Sojojin ruwa sun fara aikin hizba a Fatakwal, sun afka wa gidan karuwai, sun tserar da ‘yan mata 50

Daga WAKILINMU Kimanin ’yan mata sama da hamsin ne aka kuɓutar a gidan karuwai tare da kama wasu mutane uku da ake zargin masu safarar mutane don jima'i ne a wani samame da jami'an sojin ruwan Nijeriya suka kai a wasu gidajen karuwai biyu a Fatakwal, babban birnin Jihar Ribas. Babban Kwamanda Richard Iginla, Jami’in yaɗa labarai na sansanin sojin ruwa na NNS Pathfinder, ya bayyana hakan a ranar Lahadi ga manema labarai yayin da ya ke gabatar da waɗanda ake zargin a Fatakwal. Iginla ya ce, an gudanar da aikin ne tare da haɗin gwiwar hukumar hana fataucin mutane…
Read More
Barazanar hari: ‘Yan Birtaniya na iya ziyartar Abuja – Ofishin Jakadanci

Barazanar hari: ‘Yan Birtaniya na iya ziyartar Abuja – Ofishin Jakadanci

Daga BASHIR ISAH Gwamnatin Birtaniya ta ce yanzu 'yan ƙasar za su iya ziyartar babban birnin Nijeriya, Abuja, ba tare da wani tsoro ba. A ranar 23 ga Oktoba ƙasar ta yi gargaɗin 'ya'yanta su ƙaurace wa Abuja saboda barazanar harin ta'addanci. Ofishin Jakadancin Birtaniya da ke Abuja, ya gargaɗi 'yan ƙasar da su yi taka-tsan-tsan da zamansu a birnin na Abuja. Sai dai kuma, cikin sanarwar da ya wallafa a shafinsa na intanet a ranar Litinin da ta gabata, ofishin Jakadancin ya ce 'yan ƙasar na iya ziyartar Abuja duk da dai hadarin barazanar bai gushe ba. Amma ya…
Read More
Sojoji sun kashe shugabannin ’yan ISWAP a tafkin Chadi

Sojoji sun kashe shugabannin ’yan ISWAP a tafkin Chadi

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Rundunar Sojojin Nijeriya sun samu nasarar halaka wasu manyan shugabannin ƙungiyar ta'addancin ISWAP, Ali Kwaya da Bukar Mainoka a Tafkin Chadi. An kashe su ne a wani samame da jiragen yaƙin sojin Nojeriya suka kai a tafkin Chadi a ranar Asabar. Kwaya da Mainoka, waɗanda kuma su ne jagororin ’yan ƙungiyar ISWAP Shura (Consultation) Council sun baƙonci lahira a lokacin da Rundunar Sojan Sama na 'Operation Hadin Kai' ta gudanar da aikin ceto a Belowa, ɗaya daga cikin ’yan tsirarun da suka rage na ISWAP/Boko Haram a Tumbuns. Yankin tafkin Chadi a ƙaramar hukumar Abadam. An…
Read More
Jirgin ƙasan Abuja-Kaduna zai soma aiki kwanan nan -Minista

Jirgin ƙasan Abuja-Kaduna zai soma aiki kwanan nan -Minista

Daga BASHIR ISAH Gwamnatin Nijeriya ta ba da sanarwar ranar da jirgin ƙasar Abuja zuwa Kaduna zai dawo bayan da ya shafe watanni bakwai ba ya aiki sakamon harin 'yan ta'adda. Ministan Sufuri, Mu’azu Sambo ya ba da sanarwar hakan inda ya ce jirgin zai koma bakin aiki kwanan nan. Ya bayyana hakan ne sa'ilin da yake bayanin ayyukan da ma'aikatarsa ta aiwatar ranar Litinin a Abuja. Ya ce, cikin wannan wata na 11 jirgin zai ci gaba da aiki, tare da cewa an samar da ingantaccen tsaro don kare rayukan fasinjoji. Idan dai za a iya tunawa, Hukumar Sufurin…
Read More
Ɗan jarida na neman diyyar miliyan N100  bisa naushin da Shugaban Masu Rinjaye na Majalisar Wakilai ya yi masa

Ɗan jarida na neman diyyar miliyan N100  bisa naushin da Shugaban Masu Rinjaye na Majalisar Wakilai ya yi masa

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano A yayin da ake bikin ranar cin zarafin 'yan jarida ta duniya a duk ranar 2 ga Nuwanban kowace shekara, wani ɗan jarida a Kano ya fuskancin cin zarafin a wajen shugaban masu rinjaye na Majalisar Tarayya mai makiltar Tudun Wada da Dogowa Hon. Alasan Ado Doguwa. Lamarin dai ya faru ne bayan Doguwa ya kira taron 'yan jarida a gidansa domin maida martani akan rikicinsu da ɗan takarar Mataimakin Gwamnan Kano Hon. Murtala Sulen Garo.  Ɗan jaridar mai suna Abdullahi Yakubu na Jaridar Leadership ya garzaya kotun Gyaɗi-gyaɗi ƙarƙashin jagorancin Halima Kurawa, inda ya…
Read More
‘Yan Nijeriya ba su da hujjar kukan yunwa, inji Buhari

‘Yan Nijeriya ba su da hujjar kukan yunwa, inji Buhari

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari ya ce, 'yan Nijeriya ba su da wani dalili na yin kuka akan yunwa a lokacin da ƙasar ke da albarkacin katafarun filayen noma. Buhari ya bayyana haka ne a wata hira da ya yi da gidan talabijin na Tambari Hausa TV, wacce aka yaɗa a daren Laraba. Yayin da ya ke amsa tambaya kan yadda ake fama da yunwa a ƙasar, shugaban ya ce, duk wanda da gaske yunwar ya ke ji, to kuwa zai ɗauki kayan noma ya nufi gona. A cewarsa, rufe iyakokin ƙasa da sauran manufofin…
Read More
ASUU ta kira taron gaggawa kan shiga sabon yajin aiki

ASUU ta kira taron gaggawa kan shiga sabon yajin aiki

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Ƙungiyar Malaman Jami’'o'i (ASUU) ta kira zaman gaggawa na Majalisar Zartarwarta don yanke shawara kan shiga sabon yajin aiki. ASUU ta kiran zaman gaggawan ne sakamakon rabin albashin watan Oktoba da Gwamnatin Tarayya ta biya malaman jami’a bayan sun janye yajin aiki. Wani mamba a kwamitin zartarwar ASUU ya ce, mambobin ƙungiyar sun fusata da yanke albashin nasu da suke zargin Ministan Ƙwadago, Chris Ngige da yi. Wani jami’in ƙungiyar ya shaida wa manema labarai cewa, majiya mai tushe ce ta sanar da su cewa ministan ne ya ba da umarnin yanke albashin da aka biya…
Read More
Gwamnati ta ƙi biyan kishiyar ASUU duk da ƙin shiga yajin aiki

Gwamnati ta ƙi biyan kishiyar ASUU duk da ƙin shiga yajin aiki

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Sabuwar ƙungiyar CONUA da aka yi wa rajista domin ta zama kishiyar Ƙungiyar Malaman Jami’o’i (ASUU) ta koka kan rashin biyan albashin mambobin ƙungiyar duk da ƙin shiga yajin aikin da ƙungiyar ASUU ta dakatar. Idan za a iya tunawa, Gwamnatin Tarayya a ranar Talata, 4 ga Oktoba, 2022, ta yi rajistar ƙungiyoyin malaman jami'a guda biyu da suka haɗa da; 'Congress of Nigerian Universities Academics' (CONUA) da 'National Association of Medical and Dental Academic' (NAMDA). An yi rajistar ƙungiyoyin biyu kafin ASUU ta dakatar da yajin aikin da ta shafe watanni takwas tana yi a…
Read More