Labarai

Matawalle ya kafa sabbin dokokin tsaro 7 don yaƙi da matsalolin tsaron Zamfara

Matawalle ya kafa sabbin dokokin tsaro 7 don yaƙi da matsalolin tsaron Zamfara

Daga SANUSI MUHAMMAD a Gusau A matsayin wani mataki na ci gaba da yaƙi da matsalolin tsaro a Jihar Zamfara, Gwamnan Jihar, Dr. Mohammed Bello Matawalle, ya kafa wasu sabbin dokoki har guda bawkai waɗanda kuma aka buƙaci al'ummar Zamfara su kiyaye su don taimaka wa gwamnatin jihar wajen cimma ƙudurinta na neman ganin bayan matsalolin tsaro a jihar. Cikin wata sanarwar manema labarai da Kwamishinan 'Yan Sanda na Jihar Zamfara, CP Ayuba N. Elkanah, ya fitar a ranar Lahadi ta zayyano waɗannan dokoki da suka haɗa da: Haramta cin kasuwannin mako-mako a faɗin jihar, haramta sayar da man fetur…
Read More
Da Ɗumi-ɗuminsa: ‘Yan bindiga sun kashe ɗan gidan Sanata Ibn Na Allah, Captain Abdulkarim Na Allah a Kaduna

Da Ɗumi-ɗuminsa: ‘Yan bindiga sun kashe ɗan gidan Sanata Ibn Na Allah, Captain Abdulkarim Na Allah a Kaduna

Wasu da ake zargin 'yan bindiga ne a Kaduna, sun kashe Captain Abdulkarim Bala Na Allah, wanda shi ne babban ɗan Sanata Bala Ibn Na Allah, a gidansa da ke umar Gwandu a Malali, Kaduna. Za a yi jana'izar marigayin a maƙabartar Unguwar Sarki Kaduna. Wannan na zuwa ne ƙasa da mako guda inda wasu 'yan bindiga suka halaka Major Christopher Dator bayan sun yi garkuwa da shi sakamakon harin da suka kai makarantar horas da manyan jami'an sojoji (NDA) a Kaduna. Cikakken rahoton na nan tafe.
Read More
Gwamna Bello ya sadar da ɗaliban Islamiyyar Tegina da aka sako da iyayensu

Gwamna Bello ya sadar da ɗaliban Islamiyyar Tegina da aka sako da iyayensu

Gwamnatin Jihar Neja ta karɓi ɗaliban makarantar Islamiyyar Salihu Tanko da ke Tegina bayan da 'yan bindiga suka sako su. Gwamnatin ta karɓi ɗaliban ne a Fadar Gwamnantin Jihar da ke Minna tare da sada su da iyayensu. Wannan na zuwa kimanin sa'o'i 24 bayan da gwamnan jihar, Abubakar Sani Bello ya dawo daga rangadi na musamman da ya yi kan sha'anin tsaro don ƙarfafa wa rundunar tsaro ta haɗin gwiwa da ke aiki a jihar waɗanda suka yi nasarar fatattakar 'yan fashin daji daga yankin Mahundu. Gwamna Abubakar Sani Bello ya yi wa taron manema labarai bayani a gaban…
Read More
Gwamnatin Zamfara ta kuɓutar da ɗaliban kwalejin da aka yi garkuwa da su

Gwamnatin Zamfara ta kuɓutar da ɗaliban kwalejin da aka yi garkuwa da su

Daga SANUSI MUHAMMAD a Gusau Bayanai daga jihar Zamfara sun tabbatar da an sako ɗaliban Kwalejin Nazarin Harkokin Gona da Kimiyyar Dabbobi ta Jihar Zamfara, bayan kimanin makonni biyu da 'yan bindiga suka yi garkuwa da su daga kwalejin. A cewar Gwamna Bello Matawalle, ɗaliban sun samu 'yanci ne ranar Juma'a da taimakon wasu tubabbun 'yan bindiga a jihar. An kwashi ɗaliban zuwa Fadar Gwamnatin Jihar da ke Gusau babban birnin jihar tare da rakiyar jami'an tsaro inda gwamnan jihar tare da wasu manyan jami'an gwamnati suka karɓe su a hukumance. Idan dai ba a manta ba, a ranar 15…
Read More
Bayan shafe kwanaki 88 a hannun ‘yan bindiga, an sako ɗaliban Islamiyyar Neja

Bayan shafe kwanaki 88 a hannun ‘yan bindiga, an sako ɗaliban Islamiyyar Neja

Rahotanni daga jihar Neja, sun tabbatar da 'yan bindiga sun sako ɗaliban makarantar Islamiyyar Salihu Tanko su 70 da aka yi garkuwa da su a garin Tegina. Sakin nasu na zuwa ne bayan da suka shafe kwanaki 88 a hannun 'yan bindigar. Ya zuwa lokacin haɗa wannan labari, an ce ɗaliban suna hanyarsu ta zuwa Minna daga Kagara. Tun farko sai da aka biya 'yan bindigar Naira miliyan N50 a matsayin kuɗin fansa don dai a samu su sako yaran amma suka ƙi amincewa. An yi garkuwa da ɗaliban ne su 156 daga Islamiyyar a ranar Litinin, 30 ga Mayun…
Read More
Sufeto-Janar ya karɓi rahoton kwamitin bincike kan zargin Abba Kyari

Sufeto-Janar ya karɓi rahoton kwamitin bincike kan zargin Abba Kyari

Sufeto-Janar na 'Yan Sandan Nijeriya, IGP Usman Alkali Baba, ya karɓi rahoton kwamitin bincike kan zargin da aka yi wa DCP Abba Kyari na mu'amala da badaƙalar damfara. Shugaban kwamitin, SIP, DIG Joseph Egbunike, shi ne ya jagoranci miƙa rahoton a babban ofishin 'yan sanda da ke Abuja ran Alhamis. Sa'ilin da yake miƙa rahoton, DIG Egbunike ya miƙa godiyarsu ga IGP bisa damar da ya ba su na gudanar da wannan bincike. Tare da cewa, bayan kafa kwamitin a ranar 2 ga Agusta, 2021 ba tare da ɓata lokaci ba ya sunkuya aiki inda ya yi nasarar sauke nauyin…
Read More
Hira da Gwamna Ortom na neman janyo wa Channels TV jangwam

Hira da Gwamna Ortom na neman janyo wa Channels TV jangwam

Hukumar Watsa Labarai ta Ƙasa (NBC) ta aika wa tashar Channels TV ta takardar aikata ba daidai ba kan “kalaman harzuƙawa, rarrabuwan kai da rashin adalci” da Gwamnan Jihar Binuwai, Samuel Ortom ya yi, a shirin karin kumallo na tashar a ranar Talatar da ta gabata. NBC ta bayyana haka ne a cikin wata wasiƙa da ta aike wa gidan talabijin ɗin, mai ɗauke da kwanan wata 24 ga Agusta, 2021, wadda ta samu sa hannun Babban Daraktanta, Balarabe Ilelah. Wasiƙar ta ce, “Shirin wanda ya karɓi baƙuncin Gwamnan Jihar Binuwai, Governor Samuel Ortom, an fahimci ya ƙunshi kalaman da…
Read More
Harin Filato: Kaduna da Delta sun kwashe ɗalibansu da ke karatu a Jos

Harin Filato: Kaduna da Delta sun kwashe ɗalibansu da ke karatu a Jos

Biyo bayan yadda ake samun hare-hare a baya-bayan nan a jihar Filato, hakan ya sanya gwamnatin Jihar Kaduna ta kwashe 'yan asalin jihar da ke karatu a Jami'ar Jos da sauran manyan makarantu a jihohin da ke maƙwabtaka da jihar Filato. Sakataren Hukumar Bada Tallafin Karatu ta Jihar Kaduna, Rilwan Hassan, shi ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a wannan Alhamis, inda ya ce sun kammala kwashe ɗalibansu kaf a ƙarshen makon da ya gabata bisa umarnin Gwamnatin Jihar. A cewar Hassan, an ɗauki wannan mataki ne gudun kada ɗaliban su maƙale a Filato duba da…
Read More
Harin Filato: Gwamnati ta sake kafa dokar hana fita na sa’o’i 24 a Jos ta Arewa

Harin Filato: Gwamnati ta sake kafa dokar hana fita na sa’o’i 24 a Jos ta Arewa

Gwamnatin Jihar Filato ta sake kafa dokar hana fita na sa'o'i 24 a yankin ƙaramar hukumar Jos ta Arewa. Bayanin sake kafa dokar na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da ta fito ta hannu Daraktan Yaɗa Labarai da Hulɗa da Jama'a na Gwamna Simon Lalong, Dr Makut Macham, a ranar Laraba. Gwamnatin Filato ta ɗauki wannan mataki ne biyo bayan ƙazamin harin da aka kai a ƙauyen Yelwa Zangam wanda ya yi sanadiyyar mutuwar mutane da dama tare da jikkata wasu a Talatar da ta gabata. A cewar sanarwar, dokar hana fita na sa'o'i 24 ta soma aiki ne daga…
Read More
Lalong ya yi tir da harin Jos ta Arewa

Lalong ya yi tir da harin Jos ta Arewa

Gwamna Simon Lalong na Jihar Filato, ya yi tir da ƙazamin harin da aka kai a ƙauyen Yelwa Zangam da ke yankin Ƙaramar Hukumar Jos ta Arewa wanda ya yi sanadiyyar mutuwar mutane da dama da kuma lalata ɗimbin dukiyoyi. Gwamnan ya bayyana harin wanda aka kai cikin daren Talatar da ta gabata a matsayin dabbanci, tare da cewa tuni jami'an tsaro sun cafke wasu mutum goma da ake zargin suna da hannun a harin. Lalong ya bayyana haka ne cikin wata sanarwa ta hannu daraktansa na yaɗa labarai da hulɗa da jama'a, Dr Makut Macham, a wannan Laraba. Ya…
Read More