Labarai

Cutar korona: Nijeriya ta karɓi tallafin rigakafin AstraZeneca 699,760 daga Birtaniya

Cutar korona: Nijeriya ta karɓi tallafin rigakafin AstraZeneca 699,760 daga Birtaniya

A Talatar da ta gabata Nijeriya ta karɓi allurar rigakafin korona samfurin AstraZeneca-Oxford guda 699,760 ta hannun COVAX a matsayin tallafi daga Ƙasar Birtaniya. Muƙaddashin jakadan Birtaniya a Nijeriya, Gill Atkinson tare da sauran manyan jami'ai ne suka ya yi tarayya da shugaban Hukumar Kula da Lafiya a Matakin Farko ta Nijeriya, Dr Faisal Shuaib, wajen ƙaddamar da rigakafin. An ƙaddamar da maganin ne a ɗakin sanyi na ajiyar magunguna da ke daura da Babban Filin Jirgin Sama na Nnamdi Azikwe da ke Abuja. Rigakafin da Nijeriya ta karɓa ɗin wani ɓangare ne na rigakafin AstraZeneca ƙwaya milyan uku da…
Read More
Minista Lai ya saci jiki zuwa Amurka don ganawa da shugabannin Tiwita

Minista Lai ya saci jiki zuwa Amurka don ganawa da shugabannin Tiwita

Sahihan rahotanni sun tabbatar da Ministan Yaɗa Labarai da Raya Al'adu na Nijeriya, Lai Mohammed ya tafi Ƙasar Amurka musamman don ganawa da shugabannin kamfanin Tiwita. Cikin wani hoton bidiyo da aka yaɗa jiya Talata, an ga Minista Lai tare da Olusegun Adeyemi wanda hadimi ne na musamman kan harkokin yaɗa labarai ga ga Shugaban Ƙasa, a cikin jirgin sama na Delta Airline za su keta hazo zuwa Amurka. Idan dai za a iya tunawa a ranar 5 ga Yulin da ya gabata ne Gwamnatin Nijeriya ta haramta wa kamfanin Tiwita gudanar da harkokinsa a Nijeriya baya da Tiwita ta…
Read More
Kisan Musulmi a Rukuba: Sarkin Musulmi ya yi kira ga Gwamnatin Jihar Filato

Kisan Musulmi a Rukuba: Sarkin Musulmi ya yi kira ga Gwamnatin Jihar Filato

Daga AMINA YUSUF ALI Majalisar Addinin Musulunci ta Ƙasa a ƙarƙashin jagorancin Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Sa'ad Abubakar III (JNI) ta yi kira ga Gwanmatin Jihar Filato da ta nemo masu aika-aikar kisan Muslmin Rukuba, don a gurfanar da su. A cewar majalisar, wannan al'amari ya nuna ƙololuwar rashin wayewa inda Ƙungiyar Jama'atu Nasrul Islam ta yi kira ga gwamnatin jihar filato da ta yi gaggawar bincikowa tare da hukunta waɗanda suke da hannu acikin wannan mummunan aikin na kisan musulmi a hanyar Rakuba. A wata takardar jawabin manema labarai da ƙungiyar ta wallafa, wacce take ɗauke da sa…
Read More
INEC ta samu buƙatun rajistar zaɓe miliyan 2.4, yayin da an yi rajistar mutum miliyan 1.9 ta yanar gizo

INEC ta samu buƙatun rajistar zaɓe miliyan 2.4, yayin da an yi rajistar mutum miliyan 1.9 ta yanar gizo

Ya zuwa yanzu, Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta samu buƙatar yin rajista guda 2,449,648 daga ranar da ta fara aikin rajistar masu zaɓe (wato Continuous Voter Registration, CVR) wato 28 ga Yuni, a cewar wani jadawalin mako-mako na aikin wanda aka fitar a ranar Litinin a Abuja. Hukumar Dillancin Labarai ta Nijeriya (NAN) ta ruwaito cewa jadawalin ya kuma nuna cewa ya zuwa yanzu, 'yan Nijeriya 1,923,725 ne su ka kammala matakan farko na yin rajistar su ta hanyar yanar gizo a cikin wannan lokacin na mako bakwai a daidai ƙarfe 7 na safiyar ranar Litinin, 16 ga Agusta. Bugu…
Read More
Abin da ya sa ba mu kashe tubabbun ‘yan ta’adda, cewar sojoji

Abin da ya sa ba mu kashe tubabbun ‘yan ta’adda, cewar sojoji

Rundunar sojan Nijeriya ta ce, babban taro na duniya wanda ita ma Nijeriya ta sanya hannu a kansa, bai yarda da kashe tubabbun 'yan ta'addan da suka miƙa wuya ba. Rundunar ta faɗi haka ne a matsayin martani ga ra'ayin wasu 'yan ƙasa da ke ganin cewa me zai hana a kashe 'yan Boko Haram ɗin da suka ce sun tuba maimakon amincewa da su su ci gaba da rayuwa a cikin al'umma. MANHAJA ta kalato cewa a tsakanin watanni ukun da suka gabata, mayaƙan Boko Haram da na ISWAP sama da 3,000 ne aka damƙe ko suka tuba suka…
Read More
Tsohon mataimakin shugaban Majalisar Dattawa, Ibrahim Mantu ya kwanta dama

Tsohon mataimakin shugaban Majalisar Dattawa, Ibrahim Mantu ya kwanta dama

Allah Ya yi wa tsohon mataimakin shugaban Majalisar Dattawa, Ibrahim Nasiru Mantu. Bayanai sun nuna marigayin ya rasu ne a cikin daren Litinin a wata asibitin Abuja bayan fama da rashin lafiya. A halin rayuwarsa, marigayin cikakken ɗan siyasa ne, kuma tsohon sanata da ya wakilci Filato ta Tsakiya a Majalisar Dattawa. An zaɓe shi a matsayin sanata ne 1999 inda ya zama mataimakin shugaban Majalisar a shekarar 2000. Baya ga haka, Mantu ya yi aiki a wurare da dama tare da riƙe muƙamai daban-daban inda ya ba da tasa gudunmawa ga cigaban ƙasa. An haifi Mantu ne a ranar…
Read More
Amincewa da tubabbun ‘yan Boko Haram na iya haifar da tawaye a Borno – Zulum

Amincewa da tubabbun ‘yan Boko Haram na iya haifar da tawaye a Borno – Zulum

Gwamnan Jihar Borno, Babagana Uamara Zulum, ya bayyana cewa tubabbun 'yan Boko Haram su 1,000 da suka miƙa wuya sun bar gwamnatin jihar da al'ummarta cikin wani mawuyacin halin tsaro mai baki biyu. A cewar gwamnan, muddin gwamnati da masu faɗa a ji a jihar ba su haɗa kai sun ɗauki matakin daƙile matsalar tsaron da jihar ke fuskanta a halin yanzu ba, hakan ka iya haifar da 'yan tawayen farar hula a jihar. Zulum ya bayyana haka ne a lokacin da yake yi wa shugabannin jami'an tsaro da sarakuna jawabi a Bama da Gwoza. Ya ci gaba da cewa,…
Read More
Da Ɗumi-ɗuminsa: Buhari ya sanya hannu a kan dokar harkokin man fetur

Da Ɗumi-ɗuminsa: Buhari ya sanya hannu a kan dokar harkokin man fetur

Daga AMINA YUSUF ALI A yau Litinin, 16 ga watan Agusta, Shugaban Ƙasar Najeriya, Muhammadu Buhari, ya sanya wa ƙudurin harkokin man fetur hannu domin mai da shi doka. Bayanin haka ya fito ne daga mai bai wa Buhari shawara na musamman a kan hulɗa da jama'a da kuma watsa labarai, Femi Adesina a Abuja. Adesina ya ce hakan ya faru jim kaɗan bayan Shugaban ya dawo daga Landan a yayin da yake zaman killace kai na kwana biyar kamar yadda kwamitin tafiyar da harkokin yaƙi da annobar korona na Fadar Shugaban Ƙasa ya buƙata. Ya ce Buhari ya rattaba…
Read More