Labarai

Ku daina ziyarar alƙalai cikin dare, inji Alƙalin Kotun Ƙoli

Ku daina ziyarar alƙalai cikin dare, inji Alƙalin Kotun Ƙoli

Daga AMINA YUSUF ALI Alƙalin Kotun Ƙolin Nijeriya, Mai Shari'a Inyang Okoro, ya bayyana cewa, Sashen Shari'a na ƙasar nan ba za ta taɓa yin aikinta yadda ya kamata ba har sai ta tsira daga matsalar tauye haƙƙi daga gwamnatocin jihohi. Wanda ya haɗa da kai ziyara zuwa gidajen alƙalai domin ƙara wa miyarsu gishiri.  Okoro ya bayyana haka ranar Juma'a a garin Abuja yayin taron laccar da ƙungiyar ma'aikatan Shari'a ta Nijeriya (NBA) ta shirya mai taken: 'Tauye ikon sashen Shari'a a mulkin demokraɗiyya: Dalilansa, sakamakonsa, da kuma mafita'. Mai Shari'ar ya ƙara da cewa, in dai wannan ta'adar…
Read More
Ma’aikatu da hukumomin gwamnati sun tsaya cak sakamakon rashin sakin kasafin 2022

Ma’aikatu da hukumomin gwamnati sun tsaya cak sakamakon rashin sakin kasafin 2022

Daga AMINA YUSUF ALI A yanzu haka dai ma'aikatu, sassa da kuma hukumomin gwamnati (MDA) da kuma kamfanonin gine-gine da sauransu sun shiga matsanancin ƙarancin kuɗi a sakamakon jinkirin sakin kasafin kuɗi na shekarar 2022 da ya sa maiakatun suka tsaya cak suka kasa gudanar da manyan ayyukan raya ƙasa.  A yanzu haka Ma'aikatun da sassa da kuma hukumomin gwamnati (MDA) waɗanda su ne suka fi buƙatuwa da a saki waɗancan kuɗaɗe na kasafin wanda aka ware domin ayyukan raya ƙasa sayen kayan aiki, da sauransu, sun shiga guna-guni a kan jinkirin da aka samu na qin sakin kuɗaɗen bayan…
Read More
Badaƙalar kuɗi: Gwamna Atiku na fafutukar sasantawa da Amurka a bayan fage

Badaƙalar kuɗi: Gwamna Atiku na fafutukar sasantawa da Amurka a bayan fage

Daga JAMIL GULMA a Kebbi Gwamnan Jihar Kebbi Sanata Atiku Bagudu ya roƙi Gwamnatin Ƙasar Amurka da ta yi wa Allah ta bari a sasanta zargin badaƙalar Dalar Amurka milliyan ɗari da arba'in ($140,000,000:00), wanda ya yi daidai da Naira Billiyan Hamsin da Takwas da ɗigo Uku (#58.3b), waɗanda tsohon Shugaban Nijeriya, Marigayi Janar Sani Abacha, ya ƙetare da su zuwa ƙasashen waje, waɗansu masu bincike suka gano da hannun Gwamna Atikun dumu-dumu a ciki. Kamar yadda Jaridar Premium Times ta ruwaito a shafinta ta ce, shari'ar, wacce ke gudana tsakanin sashen shari'a na Ƙasar Amurka, (US Department of Justice, USDOJ)…
Read More
’Yan bindiga sun fasa Jihar Jigawa, sun kashe jami’in tsaro

’Yan bindiga sun fasa Jihar Jigawa, sun kashe jami’in tsaro

*Mun fatattake su zuwa cikin daji, inji ACG Abba Daga Abubakar Muhammad Tahir  ’Yan bindiga ɗauke da muggan makamai sun halaka jami'in shige da fice tare da raunata guda biyu daga cikin jami'an hukumar. Cikin wata ganawa da manema labarai da Shugaban Hukumar na Jihar Jigawa, ACG Ismail Abba, ya yi da manema labarai a ranar Laraba a Dutse, Babban Birnin Jihar ta Jigawa, ya bayyana cewa, lamarin ya faru ne da misali qarfe 11:20 na dare lokacin da ’yan bindigar suka nufo shingen bincike na hukumar da ke yankin Birniwa-Galadi. Ya ƙara da cewa, 'yan bindigar sun zo a babura…
Read More
Ɗan majalisa ya tallafa wa al’ummarsa don rage fatara

Ɗan majalisa ya tallafa wa al’ummarsa don rage fatara

Daga AMINU AMANAWA a Sakkwato A wani mataki na ƙarfafa wa da kuma tallaffa wa al'ummar ƙananan hukumomin Gwadabawa da Illela dake a Jihar Sakkwato, ɗan majalisa mai wakiltar ƙananan hukumomin Gwadabawa da Illela a Majalisar Tarayya, Abdullahi Balarabe Salame ya raba kayayyaki ga al'ummar da yake wakilta na maƙudan nairori. A cewar ɗan majalisar wannan ya zama wajibi domin rage wa al'umma raɗaɗin talauci da suke fama da shi. Salame ya ƙara da cewa tallafi ba shakka ya zama tilas kasancewar matsalar talauci da kuma rashin aikin yi ya jefa al'umma cikin ayukkan assha. Shi ma da yake magantawa…
Read More
Addu’a ce takobin dukkan ayyukan ta’addanci – Falakin Ƙaraye

Addu’a ce takobin dukkan ayyukan ta’addanci – Falakin Ƙaraye

Daga DAUDA USMAN a Legas An bayyana cewar gudanar da addu'o'i na musamman kan zaman lafiya ita ce takobin kowane irin ƙalubale da ke addabar Nijeriya. Alhaji Bature Ƙaraye kuma Falaƙin Ƙaraye, mazaunin Legas shi ne ya bayyana haka bayan kammala ɗaurin aurensa a Kano, inda aka yi addu'ar nema wa Nijeriya zaman lafiya da yalwar arziki mai amfani. Taron ɗaurin auren dai ya gudana ne a Masallacin Sheikh Jaafar da ke Unguwar Ɗorayi a cikin birnin Kano, inda ya samu halarta manyan baƙi da nesa da na kusa, haɗi da shuwagabannin majalisar Kasuwar Mile 12 da ke Legas irinsu…
Read More
Uba da ɗansa sun rasa ransu bayan sun faɗa rijiya a Kano

Uba da ɗansa sun rasa ransu bayan sun faɗa rijiya a Kano

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Wani magidanci ɗan shekara 60, Malam Bala tare ɗan sa Sunusi Bala, mai shekaru 33 sun faɗa wata tsohowar rijiya da ke Sabon Garin Bauchi, a ƙaramar hukumar Wudil, da ke cikin garin Kano, inda suka rasa rayukansu kafin a kai ga cetosu. Mai magana da yawun hukumar kashe gobara ta jihar Kano, Alhaji Saminu Abdullahi, ya tabbatar da mutuwar su ranar Laraba da ta gabata a Kano, inda ya ce uba da ɗan nasa sun rasu ne yayin da suke  ɗibar ruwa a rijiya. Sanarwar ta ce lamarin ya faru ne ranar Talata da…
Read More
2023: Sarkin Musulmi da CAN sun rattaɓa hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya

2023: Sarkin Musulmi da CAN sun rattaɓa hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammadu Sa’ad Abubakar III, da Ƙungiyar Kiristoci ta Nijeriya (CAN) sun rattaba hannu a wata yarjejeniyar zaman lafiya gabanin babban zaɓen 2023. Yarjejeniyar dai ana sa ran ta samar da zaman lafiya da kawar da fitina ta fuskar addini a lokacin zaɓen na baɗi. Manyan masu faɗa a jin biyu sun sa hannu ne a wani taron ƙoli na qasa da ƙasa kan wanzar da ’yancin addini da wata gidauniyar samar da zaman lafiya da haɗin gwiwar wasu ƙungiyoyin kare haƙƙin bil adama guda 70 suka shirya. An gudarnar da taron…
Read More
Dariye da Nyame: Ya kamata Buhari ya san cewa dukiyar Nijeriya ba ta shi ba ce – Hajiya Naja’atu

Dariye da Nyame: Ya kamata Buhari ya san cewa dukiyar Nijeriya ba ta shi ba ce – Hajiya Naja’atu

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Tsohuwar 'yar a mutum Buhari, Hajiya Naja’atu Mohammed, ta caccaki Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari akan yafe wa tsofaffin gwamnoni, Joshua Dariye na Jihar Filato da Jolly Nyame na Jihar Taraba. Daily Nigerian ta ruwaito yadda Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari a watan Afrilu ya yafe wa Dariye da Nyame tare da wasu fursinoni 157 da ke faɗin ƙasar nan. An yanke wa Dariye, wanda ya riƙe kujerar gwamnan Jihar Filato tsakanin 1999 da 2007, shekaru 14 a gidan yari saboda satar Naira biliyan 1.16, sannan an yanke wa Nyame shekaru 12 a gidan yari akan…
Read More
Hisba ta aske gashin ɗaliban da suka yi askin banza don murnar gama makaranta a Kano

Hisba ta aske gashin ɗaliban da suka yi askin banza don murnar gama makaranta a Kano

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Hukumar Hisba ta Jihar Kano, reshen Ƙaramar Hukumar Dawakin Tofa ta kai wani samame babbar Makarantar Sakandare ta Grammar da ke garin Dawakin Tofa, inda ta kama wasu ɗalibai da askin banza a kansu, domin murnar kammala karatun sakandire. Dakarun Hisba ɗin sun yi nasarar damƙe da dama daga cikin ɗaliban, waɗanda su ka yi askin da a ke wa laƙabi da "ba kwaɓa". Bayan dakarun sun kama ɗan na kamawa, wasu kuma sun tsere, sai su ka zaunar da su a harabar makarantar, inda su ka aske musu gashin tas. Wannan na ƙunshe ne…
Read More