14
Aug
Daga AMINA YUSUF ALI Alƙalin Kotun Ƙolin Nijeriya, Mai Shari'a Inyang Okoro, ya bayyana cewa, Sashen Shari'a na ƙasar nan ba za ta taɓa yin aikinta yadda ya kamata ba har sai ta tsira daga matsalar tauye haƙƙi daga gwamnatocin jihohi. Wanda ya haɗa da kai ziyara zuwa gidajen alƙalai domin ƙara wa miyarsu gishiri. Okoro ya bayyana haka ranar Juma'a a garin Abuja yayin taron laccar da ƙungiyar ma'aikatan Shari'a ta Nijeriya (NBA) ta shirya mai taken: 'Tauye ikon sashen Shari'a a mulkin demokraɗiyya: Dalilansa, sakamakonsa, da kuma mafita'. Mai Shari'ar ya ƙara da cewa, in dai wannan ta'adar…