Labarai

‘Yan sanda sun cafke ‘yan fashin intanet a Keffi

‘Yan sanda sun cafke ‘yan fashin intanet a Keffi

Daga BASHIR ISAH Rundunar 'yan sanda a garin Keffi, jihar Nasarawa, ta cafke wasu matasa su shida masu fashi a intanet da aka fi sani da 'Yahoo Boys'. Sanarwar manema labarai da rundunar ta fitar wadda ta sami sa hannun mai magana da yawun 'yan sandan jihar, ASP Ramhan Nansel, a madadin Kwamishin 'Yan Sandan Jihar, ta nuna biyo bayan bayanan sirri da rundunar ta samu game da harkokin ɓatagarin ne sai jami'anta suka yi musu dirar mikiya a maɓuyarsu da ke G.R.A Keffi inda aka kamo su. DSP Ibrahim Muhammed Siraj shi ne jami'in da ya jagoranci dakarun da…
Read More
Shugaban AMAC, Candido ya kai ziyarar ta’aziyya ga iyalan wakilin Jaridar Blueprint a Nyanya

Shugaban AMAC, Candido ya kai ziyarar ta’aziyya ga iyalan wakilin Jaridar Blueprint a Nyanya

Shugaban Hukumar AMAC ta Abuja, Hon. Abdullahi Adamu Candido, ya ziyarci iyalan marigayi Baba Yusuf, domin jajanta musu bisa rashin da ya same su. Marigayi Yusuf wanda wakilin Jaridar Blueprint ne a halin rayuwarsa, ya rasu ne ranar Talatar da ta gabata, 4 ga Agusta 2021, a gidansa da ke yankin Nyanya Gwandara a jihar Nasarawa. Kafin rasuwarsa, marigayi Yusuf mamba ne na tawagar 'yan jaridar Hukumar AMAC. Sa'ilin da yake isar da ta'aziyyarsa ga iyalan marigayin, Hon. Candido ya bayyana marigayin a matsayin ɗan jarida mai aiki tukuru daidai da dokokin aikin jarida. Haka nan, ya nuna damuwarsa kan…
Read More
Gwamnatin Zamfara ta tallafa wa iyalan ɗan jaridar da ya rasu a Kaduna

Gwamnatin Zamfara ta tallafa wa iyalan ɗan jaridar da ya rasu a Kaduna

Daga SANUSI MUHAMMAD a Gusau. Gwamnan Jihar Zamfara, Bello Matawalle, ya ba da gudunmawar kayan abinci dabam-daban da kuma kuɗi da ba a bayyana adadinsu ba ga iyalan wakilin Jaridar The Sun, Mohammed Munirat Nasir, wanda Allah Ya yi wa rasuwa a ranar Litinin da ta gabata a gidansa da ke Kaduna. Da yake gabatar da tallafin ga matar marigayin, Maryam Mohammed Munirat a madadin Gwamna a gidan marigayin da ke Kaduna a ranar Asabar, Kwamishinan Yaɗa Labarai na Jihar, Ibrahim Magaji Dosara, ya ce, "Ina fatan in gabatar da waɗannan kayan abinci a matsayin tallafi ga dangin da ya…
Read More
Kwalara ta kashe mutum 60 a Katsina

Kwalara ta kashe mutum 60 a Katsina

Aƙalla mutum 60 ne aka ruwaito sun rasu sakamakon ɓarkewar cutar amai da gudawa ko kuma kwalara, a tsakanin wasu ƙauyukan jihar Katsina. Kwamishinan lafiya na jihar, Yakubu Danja ne ya bayyana haka ranar Asabar da ta gabata a wajen taron shekara-shekara na 2021 na Ƙungiyar Likitoci ta Ƙasa (NMA) reshen jihar da ya gudana a jihar. Sai dai, Kwamishinan bai yi ƙarin bayani ba kan takamammen lokacin da aka samu rashe-rashen ba. Danja ya ce gwamnatin jihar ta ɗauki matakin gudanar da shirin wayar da kan 'yan jihar dangane da yaƙi da cutar a tsakanin ƙananan hukumomi 34 da…
Read More
Ta banka wa kanta wuta saboda tsananin kishi a Jigawa

Ta banka wa kanta wuta saboda tsananin kishi a Jigawa

Daga UMAR AƘILU MAJERI a Dutse Wata mata 'yar kimanin shekara 25 da haihuwa, ta banka wa kanta wuta saboda tsananin kishi a ƙauyen Ƙwayamawa da ke cikin ƙaramar hukumar Dutse a jihar Jigawa. Bayanan da MANHAJA ta kalato sun nuna cewa, sai da matar ta bulbule kanta da man fetur kana daga bisani ta cinna wa kanta wuta. An ce bayan da ta ga uwar-bari sakamakon raɗaɗin wutar ta ke cin ta, sai ta ruga waje tana ihu tana neman taimako, inda a nan waɗanda ke kusa suka taimaka wajen kashe wutar. Duk da dai an yi nasarar kashe…
Read More
2023: Matashi ya fi cancanta da mulkin Nijeriya – IBB

2023: Matashi ya fi cancanta da mulkin Nijeriya – IBB

A cikin wata wasiƙa da Tsohon Shugaban Ƙasa, Ibrahim Badamasi Babangida (IBB), ya aika wa jagoran APC, Bola Tinubu, da tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, ya jaddada musu cewa Nijeriya ta fi buƙatar matashin shugaba a 2023. Haka ma, ko a wata hira da aka yi da shi a tashar ARISE TV a Juma'ar da ta gabata, an ji Babangida ya ce, "Na soma hanƙoron matashin shugaba a Nijeriya." Ya ce, "Na riga da na ga mutum ɗaya ko biyu ko uku daga irin waɗannan matasa, na yi imanin za su iya muddin za mu jawo su." Atiku da…
Read More
Kotu ta yanke wa magidanci hukuncin kisa a Jigawa

Kotu ta yanke wa magidanci hukuncin kisa a Jigawa

Daga UMAR AƘILU MAJERI a Dutse Wata Babbar Kotun Jihar Jigawa mai zamanta a garin Gumel, ta zartar da hukuncin kisa ta hanyar rataya a kan wani mai suna Rabi’u Mamman. Sanarwar Daraktan Sashin Ayyuka na Musamman da Harkokin Baƙi na Ɓangaren Shari’a na jihar Jigawa, Malam Abbas Rufa’i Wangara, ya sanya wa hannu ta ce, kotun ƙarƙashin jagoranci Mai Shari’a Abubakar Sambo Muhammad ta sami Mamman da aikata kisan kai wanda ya saɓa wa sashi na 221(B) na kundin Penal code. Kotun ta samu Rabi’u Mamman da ke garin Medinlaban a yankin ƙaramar hukumar Gagarawa da ɓoye kansa a…
Read More
Kotu ta tura ɗan gidan tsohon Shugaban Ƙasa Yar’aduwa kurkuku kan zargin halaka mutum huɗu a Yola

Kotu ta tura ɗan gidan tsohon Shugaban Ƙasa Yar’aduwa kurkuku kan zargin halaka mutum huɗu a Yola

An ingiza ƙeyar ɗan gidan tsohon Shugaban Ƙasa, Umaru Musa Yar’adua, Aminu Yar’adua, zuwa kurkuku a Yola, jihar Adamawa bisa zargin murƙurshe mutum huɗu har lahira da mota. Aminu Yar’adua, ɗan shekara 36, ɗalibi ne a Jami'ar Amurka da ke Nijeriya (AUN), wata kotun Majatare ƙarƙashin jagoranci Alƙali Jummai Ibrahim ta ba da umarnin a kai shi kurkuku a Alhamis da ta gabata bisa zargin kashe mutum huɗu da mota. An maka aminu a kotu ne bisa tuhumar yin ajalin wasu mutum huɗu sakamakon mummunan tuƙin da ya yi a ranar 23 ga Yunin 2021. Bayanan farko da 'yan sanda…
Read More
‘Yan bindiga sun yi garkuwa da iyayen Kakakin Majalisar Zamfara

‘Yan bindiga sun yi garkuwa da iyayen Kakakin Majalisar Zamfara

Daga SANUSI MUHAMMAD a Gusau Rundunar 'yan sandan jihar Zamfara ta tabbatar da yin garkuwa da mahaifi da kishiyar mahaifiyar Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Zamfara, Hon. Nasiru Muazu Magarya, a wani hari da 'yan bindigar suka kai a ƙauyen Magarya da ke cikin ƙaramar hukumar Zurmi a jihar Mai magana da yawun rundunar, SP Shehu Muhammd, shi me ya tabbatar da faruwar lamarin tare da cewa Kwamishinan ‘Yan Sandan Jihar, Hussaini Rabiu ya tura isassun jami'an tsaro da nufin ceto mutanen da aka sace. Sai dai wani mazaunin yankin mai suna Muhammadu Lawali, ya shaida wa wakilin MANHAJA ta waya…
Read More