07
Aug
Daga AMINU AMANAWA a Sakkwato Ɗan takarar shugabancin Nijeriya na Jam'iyyar PDP a zaɓen 2023 kuma tsohon mataimakin shugaban ƙasa Atiku Abubakar ya bai wa matasan Nijeriya tabbacin barin kyakkyawan tarihi gare su, idan aka ba shi damar jagorantar al'amuran ƙasar. Atiku Abubakar ya bada wannan tabbaci ne lokacin da ya karvi baƙuncin tawagar shugannin PDP sabon ƙarni ƙarƙashin jagorancin babban daraktan ta Audu Mahmud a gidansa dake Abuja. Ɗan takarar shugabancin ƙasar ya sake jaddada aniyarsa kamar yadda ta ke ƙunshe cikin kundin manufofinsa, na bai wa matasa dama a gwamnatinsa ta hanyar ware musu kaso 40, inda kuma…