Labarai

2023: Zan bada kaso 40 na muƙamai ga matasa da mata – Atiku

2023: Zan bada kaso 40 na muƙamai ga matasa da mata – Atiku

Daga AMINU AMANAWA a Sakkwato Ɗan takarar shugabancin Nijeriya na Jam'iyyar PDP a zaɓen 2023 kuma tsohon mataimakin shugaban ƙasa Atiku Abubakar ya bai wa matasan Nijeriya tabbacin barin kyakkyawan tarihi gare su, idan aka ba shi damar jagorantar al'amuran ƙasar. Atiku Abubakar ya bada wannan tabbaci ne lokacin da ya karvi baƙuncin tawagar shugannin PDP sabon ƙarni ƙarƙashin jagorancin babban daraktan ta Audu Mahmud a gidansa dake Abuja. Ɗan takarar shugabancin ƙasar ya sake jaddada aniyarsa kamar yadda ta ke ƙunshe cikin kundin manufofinsa, na bai wa matasa dama a gwamnatinsa ta hanyar ware musu kaso 40, inda kuma…
Read More
Bankin Duniya da Hukumar Ƙidaya sun horar da ’yan jarida kan yawan al’umma don inganta rayuwa

Bankin Duniya da Hukumar Ƙidaya sun horar da ’yan jarida kan yawan al’umma don inganta rayuwa

Daga NASIR S. GWANGWAZO a Legas Bankin Duniya da Hukumar Ƙidaya ta Nijeriya (NPC) sun shirya wa wasu zaɓaɓɓun ’yan jarida horarwa kan kula da yawan al’umma, don inganta rayuwar ’yan Nijeriya. An shirya horon na kwana uku ne a otel ɗin Lagos Intercontinental da ke Birnin Ikko a ranakun Litinin, 17 zuwa Laraba, 21 ga Yuli, 2022. A ranar Litinin an fara da gabatar da maƙasudin taron ne, inda shugabannin jami’an Bankin Duniya da na Hukumar NPC suka gabatar da jawabai tare da tattaunawa da mahalarta taron kan alƙiblar da ta kamata ’yan Nijeriya su sanya a gaba kan…
Read More
Ƙungiyar NAF ta yi martani ga matasan Arewa masu yekuwar a tsige Janar Monguno

Ƙungiyar NAF ta yi martani ga matasan Arewa masu yekuwar a tsige Janar Monguno

Daga NASIR S. GWANGWAZO a Abuja Ƙungiyar Arewa Ina Mafita ta yi kakkausan martani ga wata ƙungiyar matasan arewa mai suna ‘Arewa Youth Assembly bisa kira da suka yi na murabus ɗin mai ba shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsrao, Janar Babagana Mongonu. Rahotanni sun ruwaito kakakin ƙungiyar, Mohammed Danlami ne ya yi wannan kira a wata takardar sanarwar manema labarai da ya rattaba wa hannu a ranar Litinin ɗin da ta gabata, inda ƙungiyar tasu ta nemi Janar Monguno da ya yi ritaya ko Shugaba Buhari ya tsige shi. Sai dai a yayin mayar da martani ga wannan matsaya…
Read More
Atiku ya naɗa Dino Melaye da Daniel Bwala a matsayin kakakinsa

Atiku ya naɗa Dino Melaye da Daniel Bwala a matsayin kakakinsa

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP kuma tsohon mataimakin shugaban ƙasar Nijeriya, Atiku Abubakar ya naɗa Sanata Dino Melaye da Dakta Daniel Bwala a matsayin masu magana da yawun ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a yaƙin neman zaven shugaban ƙasa mai zuwa. A cewar sanarwar da mai baiwa Atiku shawara kan harkokin yaɗa labarai, Paul Ibe ya sanyawa hannu, naɗin na biyu ya fara aiki nan take. Malaye ɗan siyasa ne kuma ɗan majalisar dattawa ta 8, wanda ke wakiltar mazaɓar Kogi ta Yamma. Ya fito daga Ayetoro Gbede da ke ƙaramar hukumar…
Read More
Rundunar Sojojin Nijeriy ba ta ɓangaranci ce ba – Janar Ali

Rundunar Sojojin Nijeriy ba ta ɓangaranci ce ba – Janar Ali

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Manjo Janar Ibrahim Ali, Kwamandan Operation Safe Heaven (OPSH) mai wanzar da zaman lafiya a Filato da kewaye, ya ce, sojoji za su kasance na al’umma da kuma yin adalci ga kowa wajen tabbatar da tsaron ƙasa. Kamfanin Dillancin Labaran Nijeriya (NAN) ya ruwaito cewa, tawagar ta OPSH tawaga ce da ke da alhakin tabbatar da tsaro da rayuka da dukiyoyi a Filato da Bauchi da kuma wasu sassan kudancin Kaduna. An kafa ta ne a shekarar 2010 kuma ta ƙunshi Sojojin Nijeriya na Ruwa, Sama, Jami'an ’yan sanda, jami'an NSCDC da jami'an tsaro na farin…
Read More
Ya kamata gwamnati ta ƙara wa’adin rajistar zaɓe, cewar ’Yar takarar kansila a Sakkwato

Ya kamata gwamnati ta ƙara wa’adin rajistar zaɓe, cewar ’Yar takarar kansila a Sakkwato

Daga AMINU AMANAWA a Sakkwato An bayyana buƙatar da ke akwai ga Gwamnatin Tarayya da ta duba yuwar ƙara wa'adin ci gaba da rajistar masu zaɓe, da hukumar INEC ta dakatar. Wata 'yar takarar kansila a mazaɓar Sanyinnan dake Ƙaramar Hukumar mulkin Tanmbuwal Hajiya Daraja Shehu Sanyinnan ce ta yi wannan kiran cikin wani bayani da ta fitar. Ta bayyana cewa ƙara lokacin rajistar masu zaɓen zai bayar da dama ga waɗanda suka kai munzalin jefa ƙuri'a yankar rijistar domin su samu damar jefa ƙuri'a a babban zaɓen gamagari da ke tafe. Haka ma Daraha Shehu ya yaba wa matar…
Read More
Sakkwato za ta kashe Naira biliyan 12 wajen sanya na’urorin kiwon lafiya a asibitin koyarwar jihar

Sakkwato za ta kashe Naira biliyan 12 wajen sanya na’urorin kiwon lafiya a asibitin koyarwar jihar

Daga AMINU AMANAWA a Sakkwato Gwamnatin Jihar Sakkwato ta bayyana cewa a mako mai zuwa ne za a soma sanya kayan aiki ga asibitin koyarwa ta Jami'ar jihar. Kwamishinan Lafiya na Jihar Sakkwato Dr. Ali Mohammad Inname ne ya sanar da haka a yayin gudanar da wani taro da wakilan kamfanin da aka bai wa aikin Thomat Company Nigeria Ltd, taron da ya gudana a harabar asibitin. Dr. Muhammad Ali Inname, ya ce wannan ya biyo bayan amincewar Gwamna Aminu Waziri Tambuwal na cefano kayakin tare da sanya su, kuɗin da suka kai kimanin Naira Biliyan 12. A cewarsa, za…
Read More
Harin jirgin ƙasa: Har yanzu ni masoyin Buhari ne, inji fasinjan da ya kuɓuta

Harin jirgin ƙasa: Har yanzu ni masoyin Buhari ne, inji fasinjan da ya kuɓuta

Daga SANI AHMAD GIWA Ɗaya daga cikin mutanen da suka kuɓuta daga hannun 'yan bindigar jirgin ƙasan Abuja zuwa Kaduna, Barista Hassan Usman, ya ce har yanzu shi masoyin Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ne. A ranar 28 ga watan Maris, wasu ‘yan bindiga suka kai hari kan wani jirgin ƙasa da ke kan hanyar Kaduna, inda aka kashe mutane da dama, aka kuma yi awon gaba da wasu. Hassan na daga cikin fasinjoji huɗu da aka sako daga hannun masu garkuwar a ranar 25 ga watan Yuli. Da yake magana a wata hira da ICIR, ya ce duk da cewa…
Read More
2023: INEC za ta yi amfani da dokokin zaɓe ba tare da tsoro ba – Yakubu

2023: INEC za ta yi amfani da dokokin zaɓe ba tare da tsoro ba – Yakubu

Daga SANI AHMMAD GIWA a AbujaHukuma Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa, INEC, za ta yi taka-tsan-tsan wajen aiwatar da dokoki, musamman Dokar Zaɓe ta 2022, ba tare da tsoro ko son rai ba, don tabbatar da sahihin zaɓe, gaskiya da adalci a 2023. Shugaban hukumar ta INEC, Farfesa Mahmood Yakubu ne ya bayyana haka a ranar Laraba a Abuja, a wajen taron tunawa da Marigayi Darakta Janar na Cibiyar Zaɓe, TEI, Farfesa Abubakar Momoh, wanda ya rasu a ranar 29 ga Mayu, 2017. Mista Yakubu ya samu wakilcin Farfesa Abdullahi Zuru, kwamishinan ƙasa kuma shugaban hukumar zaɓe ta ƙasa.…
Read More
‘Yan sanda za su fara kai samame dazuka da gine-ginen da ba kowa a Abuja

‘Yan sanda za su fara kai samame dazuka da gine-ginen da ba kowa a Abuja

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja 'Yan sandan Birnin Tarayyar Nijeriya Abuja sun fara hai samame dazuzzuka da gine-ginen da babu kowa a cikin gari da unguwannin bayan gari. Mai magana da yawun rundunar 'yan sandan Josephine Adeh ne ya faɗi hakan a ranar Laraba, kamar yadda kafar yaɗa labaran Channel ta ruwaito. A yayin da take ƙaryata jita-jitar cewa akwai mafakar masu garkuwa da mutane a cikin Abuja, ta ce a kwanaki masu zuwa mazauna birnin za su ga an tsaurara matakan tsaro. Harin ya zo ne ƙasa da sa'a 24 ba bayan da rundunar 'yan sanda ta yi…
Read More