Labarai

Ƙarin kuɗin lantarki: Mataimakin Kakakin Majalisar Wakilai ya sha alwashin duba lamarin

Ƙarin kuɗin lantarki: Mataimakin Kakakin Majalisar Wakilai ya sha alwashin duba lamarin

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Mataimakin Kakakin Majalisar Wakilai, Benjamin Kalu, ya kwantarwa da ’yan Nijeriya hankali kan batun ƙarin farashin wutar lantarki da Gwamnatin Tarayya ta yi. Ben Kalu ya ce 'yan majalisar sun ƙudiri aniyar tafka muhawara kan ko ya kamata a yi ƙarin kuɗin wutar ko a'a. A cewar mai magana da yawun Kalu, Levinus Nwabughiogi, ɗan majalisar na amsa tambayar wani mai sauraro da ya yi kiran waya cikin shirin yana tambayar matsayar majalisa kan ƙarin kuxin wutar. Kalu ya ce, "Gama-garin matsala ce. Ina cikin hutu, amma daga abin da ke damu na akwai takardar da…
Read More
EFCC ta ƙwato Naira Biliyan 30 yayin binciken Better Edu

EFCC ta ƙwato Naira Biliyan 30 yayin binciken Better Edu

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Hukumar Yaƙi da Masu yi wa Tattalin Arzikin Ƙasa Tu'annati, EFCC, ta ce ta kwato wa Gwamnatin Tarayya Naira Biliyan 30, yayin da ta kuma sanya asusun ajiyar banki 50 a binciken da ake yi wa tsohuwar ministar harkokin jinqai da yaƙi da fatara, Betta Edu da wata ma’aikaciyar ma’aikatar, Halima Shehu. Kimanin watanni uku da suka gabata ne shugaba Bola Tinubu ya dakatar da Betta Edu da Halima Shehu saboda zargin karkatar da maƙuden kuɗaɗe. Nan take kuma, Shugaban ya dakatar da shirin na Tallafi da rage talauci (NSIP), sannan ya buƙaci hukumar EFCC da…
Read More
’Yan bindiga sun bi Sarkin Musulmi ranar sallah

’Yan bindiga sun bi Sarkin Musulmi ranar sallah

*Sun miƙe ƙafa a bainar jama’a Daga NASIR S. GWANGWAZO a Abuja Wasu dandazon ’yan ta'addar daji sun miƙe ƙafa a lokacin Ƙaramar Sallah da a ka gudanar ranar Larabar da ta gabata, inda suka fito suka gudanar da sallar idi tare da sauran bukukuwa a bainar jama'a a Jihar Zamfara da ke yankin Arewa Maso Yammacin Najeriya. Bikin sallar ’yan bindigar daji ya zo ne a daidai lokacin da wasu malamai su ka bijire wa umarnin Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Sa’ad Abubakar III, na sauke azumin watan Ramadan a ranar Laraba. Sarkin Musulmi ya sanar da cewa, ba…
Read More
Wulaƙanta Naira ta janyo wa ɗan daudu, Bobrisky zaman kuruku na wata shida

Wulaƙanta Naira ta janyo wa ɗan daudu, Bobrisky zaman kuruku na wata shida

Daga BASHIR ISAH Labarin da muka samu yanzu-yanzu na nuni da cewa, ɗan daudun nan Idris Olanrewaju Okuneye wanda aka fi sani da Bobrisky, zai shafe wata shida a kurkuku ba tare da wani zaɓi ba bayan da kitu ta kama shi da laifin wulaƙanta takardun kuɗi na Naira. Mai shari'a Abimbola Awogboro na Babbar Kotun Tarayya da ke Legas ce ta yanke wannan hukunci. Alƙalin ta ce hakan zai zama darasi ga sauran jama'a waɗanda ke da ɗabi'ar wulaƙanta Naira.
Read More
Tinubu ya nuna alhini kan rasuwar Saratu Giɗaɗo

Tinubu ya nuna alhini kan rasuwar Saratu Giɗaɗo

Daga BASHIR ISAH Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya nuna alhininsa dangane da rasuwar jaruma a masana'antar shirya finafinai ta Kannywood, Saratu Giɗaɗo wadda aka fi dani da Daso. Hakan na ƙunshe ne cikin sanarwar da Fadar Shugaban Ƙasa ta fitar mai ɗauke da kwanan wata 10 ga Afrilu da kuma sa hannun mai magana da yawun Shugaban Ƙasa, Ajuri Ngelale. Tinubu ya yi amfani da wannan dama wajen miƙa ta'aziyya ga 'yan uwan da abobakan aiki da masoyan marigayiyar da ke sassa daban-daban. Tinubu ya bayyana rasuwar jarumar mai shekara 56 a matsayin babban rashi ga ƙasa baki ɗaya. Ya…
Read More
Kuɗin lantarki: Ma’aikatan lantarki sun yi barazana shiga yajin aiki a Zamfara

Kuɗin lantarki: Ma’aikatan lantarki sun yi barazana shiga yajin aiki a Zamfara

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Ƙungiyar Ma’aikatan Wutar Lantarki ta Ƙasa ta yi kira da a sake nazari a kan ƙarin kuɗin wutar lantarkin da aka yi a baya-bayan nan, inda ta yi barazanar shiga yajin aiki. A cikin wata sanarwa, shugaban ƙungiyar, Adebiyi Adeyeye, ya yi gargaɗin yiwuwar shiga yajin aikin matuƙar ba a sauya ba. Hukumar da ke sa ido kan wutar lantarki ta Nijeriya ta kara haraji ga kwastomomin da ke samun wutar lantarki na sa’o’i 20 a kullum, lamarin da ya haifar da ƙarin farashin.  Adeyeye ya bayyana rashin daidaiton tsarin a matsayin hanyar da ke kashe…
Read More
Gwamnatinmu za ta ci gaba da cika alƙawurran da ta ɗaukar wa al’umma —Gwamna Abba

Gwamnatinmu za ta ci gaba da cika alƙawurran da ta ɗaukar wa al’umma —Gwamna Abba

Ya ce duk wanda zai kawo mana tashin hankali a jihar Kano hukuma za ta yi aiki kansa Daga RABIU SANUSI a Kano Gwamna Abba Kabir Yusuf na jihar Kano ya bayyana ƙudurin gwamnatinsa na cigaba da cika alƙawarin da ya yi wa al'ummarsa yayin neman zaɓe na bambaɗa musu ayyukan more rayuwa. Gwamna ya bayyana haka ne a ranar Ƙaramar Sallah yayin aike wa al'ummar jihar da ma ƙasa baki ɗaya da saƙon goron sallah. Ya ce, daga lokacin da gwamnatinsa ta karɓi ragamar mulki zuwa yanzu, sun aiwatar da ayyuka da daman gaske. Daga nan, ya ƙara jaddada…
Read More
Basarake ya kwanta dama bayan kammala  Sallar Idi a Legas

Basarake ya kwanta dama bayan kammala Sallar Idi a Legas

Daga BASHIR ISAH Allah Ya yi wa Sarkin Masarautar Isolo da ke Jihar Legas, Oba Kabiru Agbabiaka, Adeola Olushi III, rasuwa. Majiyarmu ta ce basaraken ya rasu ne a ranar Laraba jim kaɗan bayan da ya dawo daga sallar Idi. Shugaban Yankin Rayawa na Isolo (LCDA), Olasoju Adebayo, ya tabbatar da mutuwar basaraken. Ya ce za a yi jana'izar marigayin da misalin ƙarfe 4 na yamma daidai da karantarwar Islama. “Na samu umarnin Gwamman Legas, Mr. Babajide Sanwo-Olu, kan in sanar da rasuwar Sarkin Masarautar Isolo, Oba Kabiru Agbabiaka, Adeola Olushi III, a yau 10 ga Afrilun 2024. Ya rasu…
Read More
Ƙaramar Sallah: Gwamnan Zamfara ya miƙa saƙon goron sallah ga al’ummar Musulmi

Ƙaramar Sallah: Gwamnan Zamfara ya miƙa saƙon goron sallah ga al’ummar Musulmi

*Ya buƙaci a yi wa ƙasa addu'ar zaman lafiya Daga BASHIR ISAH Gwamna Dauda Lawal na Jihar Zamfara, ya taya al'ummar Musulmi murnar bikin Ƙaramar Sallah, tare da kira kan yi wa Zamfara da ma ƙasa baki ɗaya addu'ar samun dauwamammen zaman lafiya. Lawal ya miƙa saƙon nasa ne cikin sanarwar da Kakakinsa, Sulaiman Bala Idris, ya fitar. Sanarwar ta ce watan Ramadan da ya ƙare ya bai wa 'yan ƙasa damar zazzaga wa ƙasa addu'o'in samun zaman lafiya da kuma kwaranyewar matsalolin tsaron da ƙasa ke fama da su. Ta ƙara da cewa, yana da kyau Musulmi su ci…
Read More