07
Dec
Daga WAKILINMU Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya (MƊD), Antonio Guterres, ya rubuta wasiƙa ga kwamitin tsaro na majalisar, inda ya nemi ƴan kwamitin su taimaka don kauce wa mummunar annoba a Gaza. "Yayin da ake fuskantar shiga bala'in rasa agaji a Gaza, ina neman Kwamatin ya taimaka wajen kauce wa aukuwar bala'i, kuma ya nemi a tsagaita wuta don kai agaji," in ji Guterres a cikin wani saƙo da ya walafa ranar Laraba. Cikin wasiƙar da ya rubuta, Guterres ya nanata cewa yanayin na ƙara ƙazancewa cikin sauri, ta yadda ba za a iya gyara wa Falasɗinawa komai ba…