Labarai

Za a shiga mummunan bala’i a Gaza idan ba ku ɗauki mataki ba – MƊD

Za a shiga mummunan bala’i a Gaza idan ba ku ɗauki mataki ba – MƊD

Daga WAKILINMU Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya (MƊD), Antonio Guterres, ya rubuta wasiƙa ga kwamitin tsaro na majalisar, inda ya nemi ƴan kwamitin su taimaka don kauce wa mummunar annoba a Gaza. "Yayin da ake fuskantar shiga bala'in rasa agaji a Gaza, ina neman Kwamatin ya taimaka wajen kauce wa aukuwar bala'i, kuma ya nemi a tsagaita wuta don kai agaji," in ji Guterres a cikin wani saƙo da ya walafa ranar Laraba. Cikin wasiƙar da ya rubuta, Guterres ya nanata cewa yanayin na ƙara ƙazancewa cikin sauri, ta yadda ba za a iya gyara wa Falasɗinawa komai ba…
Read More
Harin bom: Shettima ya ziyarci Kaduna don jajanta wa al’ummar Tudun Biri

Harin bom: Shettima ya ziyarci Kaduna don jajanta wa al’ummar Tudun Biri

Daga BASHIR ISAH Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima, ya ziyarci Jihar Kaduna domin jajanta wa 'yan uwan waɗanda harin bom da sojoji suka kai bisa kuskure ya rutsa da su a yankin Tudun Biri a jihar. Gwamnan Kaduna, Sanata Uba Sani da sauran manyan jami'an gwamnati ne suka tarbi Mataimakin Shugaban Ƙasar bayan da ya sauka a barikin sojojin saman da ke Mando. Tawagar da ta yi wa Shettima rakiya zuwa Kaduna a ranar Alhamis ta ƙunshi Kakakin Majalisar Wakilai, Abbas Tajuddeen, Ministan Tsaro, Mohammed Badaru Abubakar; Shugaban APC na Ƙasa, Dr Abdullahi Umar Ganduje da dai sauransu. Ziyarar Shettima…
Read More
BESDA: Gwamna Lawal ya jagoranci tawaga zuwa taron bita a Rwanda

BESDA: Gwamna Lawal ya jagoranci tawaga zuwa taron bita a Rwanda

Daga BASHIR ISAH Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya jagoranci tawaga ta musamman zuwa Kigali don taron bita na yini huɗu a matsayin ɓangare na kammala shirin ba da nagartaccen ilimi na Better Education Service Delivery for All (BESDA) a jihar. Bitar mai ƙunshe da ayyuka daban-daban, an soma ta ne daga ranar Litinin, 4 ga Disamba, da zummar farfaɗo da fannin ilimin Jihar Zamfara. Mai magana da yawun Gwamna, Sulaiman Bala Idris, ya bayyana a cikin sanarwar da ya fitar cewa, shirin BESDA shiri ne na Bankin Duniya wanda aka ƙirƙiro da nufin bunƙasa sha'anin ilimi da kuma bai…
Read More
An buƙaci Tinubu ya tsige shugabannin tsaro biyo bayan harin bom a Kaduna

An buƙaci Tinubu ya tsige shugabannin tsaro biyo bayan harin bom a Kaduna

Daga BASHIR ISAH Ƙungiyar Dattawan Arewa (NEF) ta yi kira da a tsige manyan shugabannin sojoji kan harin bom da sojoji suka kai bisa kuskure a Tudun Biri, Jihar Kaduna, wanda hakan ya salwantar da rayuka sama da 85 tare da jikkata wasu da dama. Mai sharhi kan al'amuran yau da kullum kuma mamba a ƙungiyar NEF, Farfesa Usman Yusuf, shi ne ya yi wannan kira yayin wata tattaunawa da aka yi da shi a tashar Channels Television a ranar Talata. Yusuf said, “Wannan rashin dacewa ne. Dukkansu za yi murabus, a kori duk wani jami'in da ke daga cikin…
Read More
Harin Tudun Biri: Matasa sun gudanar da zanga-zangar nuna ɓacin rai a Kaduna

Harin Tudun Biri: Matasa sun gudanar da zanga-zangar nuna ɓacin rai a Kaduna

Daga BASHIR ISAH Wasu mata a garin Zariya, Jihar Kaduna, sun gudanar da zanga-zangar lumana domin nuna ɓacin ransu dangane da harin soji da ya faɗa kan masu maulidi a ƙauyen Tudun Biri da ke Ƙaramar Hukumar Igabi a jihar. An ga masu zanga-zangar sun yi tattaki a cikin garin na Zaria ɗauke da kwalaye masu ɗauke da saƙonni daban-daban kamar; "Adalci ga Arewa", "Adalci ga Igabi" da sauransu. Sama da mutum 80 ne suka mutu sannan wasu da dama sun tagayyara sakamakon harin da sojoji suka jefa bom har sau biyu ta hanyar amfani da jirgin sama mara matuƙi…
Read More
Bakwai cikin 10 na matasan Nijeriya na harkar ‘Yahoo Yahoo’ – EFCC

Bakwai cikin 10 na matasan Nijeriya na harkar ‘Yahoo Yahoo’ – EFCC

Daga BASHIR ISAH Shugaban Hukumar Yaƙi da Rashawa (EFCC), Ola Olukoyede, ya ce abin damuwa ne matuƙa yadda ake samun da yawan matasan Nijeriya na shiga harkar damfara a intanet. Olukoyede ya bayyana a cikin wata sanarwa da EFCC ta wallafa a shafinta na X cewa, wannan bala'in ya kai matsayin da a yau, a cikin kowane 10 na ɗaliban Nijeriya za a tarar da 7 daga ciki suna ta'ammali da harkar damfara ta intanet. Ya nuna damuwarsa kan wannan batu ne a lokacin da ya karɓi baƙuncin tawagar kamfanin Daar Communication PLC da suka kai ziyarar aiki a ofishinsa…
Read More
Harin Tudun Biri: Adadin waɗanda suka mutu ya kai 126

Harin Tudun Biri: Adadin waɗanda suka mutu ya kai 126

*Sau biyu sojoji na jefa mana bom, in ji wasu da suka tsira Daga BASHIR ISAH Kawo yanzu, adadin waɗanda suka mutu a harin kuskuren da sojoji suka kai Tudun Biri, cikin Ƙaramar Hukumar Igabi, Jihar Kaduna, ya kai 126. An tabbatar da hakan ne a lokacin da jami'an ƙungiyar Amnesty International suka ziyarci waɗanda harin ya shafa a ranar Talata. Wasu da suka tsira daga harin sun bayyana cewa, sau biyu sojojin na jefa musu bom. A ranar Lahadin da ta gabata wani harin bom da sujoji suka yi nufin kaiwa a kan 'yan ta'adda ya kuskure ya faɗa…
Read More
Ministan Labarai zai shugabanci taron SAEMA/SCA na 2023

Ministan Labarai zai shugabanci taron SAEMA/SCA na 2023

Daga BASHIR ISAH Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai shi ne zai shugabanci taron SAEMA karo na biyar da za a yi haɗe taron SCA karo na uku wanda zai gudana ranar Alhamis, 7 ga Disamban 2023. Bayanin haka na ƙunshe ne cikin sanarwar taron da aka yaɗa. Sauran manyan jami'an da za su haskaka taron kamar yadda sanarwar ta nuna, sun haɗa da: Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara Kan Saha'anin Tsaro (NSA), Malam Nuhu Ribadu; Shugaban NIPR, Dr. Ikeliaku; Babban Daraktan NITDA, Malam Kashifu Inuwa Abdullahi da dai sauransu. Taron wanda zai tattauna rawar da sadarwa ke…
Read More
Dubai: Mutum 422 aka ɗauki nauyinsu zuwa taron COP-28 – Malagi

Dubai: Mutum 422 aka ɗauki nauyinsu zuwa taron COP-28 – Malagi

Daga BASHIR ISAH Gwamnatin Tarayya ta maida martani kan ce-ce-ku-cen da ke yi game da adadin mutanen da ta ɗauki nauyi zuwa babba taron COP-28 da ke gudana a Dubai. Rahotanni sun ce tawagar Nijeriya na ɗaya daga cikin tawagogin da suka fi yawan mambobi da suka halarci taron wadda ke ƙunshe da mutum sama da 1000. Sai dai a ƙarin hasken da ya yi game da wannan batu, Ministan Labarai da Wayar da da Kan 'Yan Ƙasa, Mohammed Idris Malagi, ya ce, "Mutum 422 ne Gwamnatin Tarayya ta ɗauki nauyinsu zuwa wurin taron", amma ba sama da 1000 kamar…
Read More
HOTUNA: Babban Hafsan Sojoji ya jagoranci yi wa waɗanda suka mutu a harin Kaduna addu’a

HOTUNA: Babban Hafsan Sojoji ya jagoranci yi wa waɗanda suka mutu a harin Kaduna addu’a

Babban Hafsan Hafsoshin Sojin Nijeriya, Lt. General Taoreed Lagbaja, ya jagoranci yin addu'a ga gomman waɗanda suka rasa rayukansu a harin kuskuren da jirgin saman soji mara matuƙi ya kai a Tudun Biri cikin Ƙaramar Hukumar Igabi, Kaduna a ranar Lahadi. Rundunar Sojojin Nijeriya Nijeriya ta ɗauki alhakin kai harin, inda ta ce hakan ya faru ne a bisa kuskure. Ga ƙarin hotuna:
Read More