Kasashen Waje

An ga watan Ƙaramar Sallah a Nijar

An ga watan Ƙaramar Sallah a Nijar

Daga BASHIR ISAH Hukumomi a Jamhuriyar Nijar sun ce an ga watan Ƙaramar Sallah a wasu jihohi biyar na ƙasar. Don haka, Talata take 1 ga Shawwal kuma ranar Ƙaramar Sallah a ƙasar. Sai dai, maƙwabciyar Nijar, wato Nijeriya da Saudiyya da sauransu, aun ce ba su ga wata ba, wanda hakan ya sa za su yi azumi 30 a ƙasashen sannan Laraba su yi Ƙaramar Sallah.
Read More
Da Ɗumi-ɗumi: Laraba Saudiyya za ta yi Ƙaramar Sallah

Da Ɗumi-ɗumi: Laraba Saudiyya za ta yi Ƙaramar Sallah

Daga BASHIR ISAH Ƙasar Saudiyya ta bayyana cewa, ya zuwa ranar Laraba, 10 ga watan Afrilun 2024 za a yi Ƙaramar Sallah a ƙasar. Ta ce hakan ya faru ne sakamakon rashin ganin jinjirin watan Shawwal a ranar Litinin wanda hakan ya sa za a yi azumin Ramadan 30 a ƙasar. Kafin wannan lokaci, masana da masu bincike a fagen ilimin taurari sun ce da wahala a ga jinjirin watan Shawwal a ranar Litinin saboda yanayin tafiyar duniyar wata da ta rana. Da wannan, ya tabbata Laraba ce 1 ga watan Shawwal, 1445AH a ƙasar Saudiyya.
Read More
Da Ɗumi:ɗumi: An rantsar da Bassirou Faye a matsayin sabon Shugaban Ƙasar Senegal

Da Ɗumi:ɗumi: An rantsar da Bassirou Faye a matsayin sabon Shugaban Ƙasar Senegal

*Ya zama Shugaban Ƙasa mafi ƙarancin shekaru a Afirka Daga BASHIR ISAH An rantsar da Bassirou Diomaye Faye a matsayin sabon zaɓaɓɓen Shugaban Ƙasa don ci gaba da jan ragamar mulkin ƙasar. Da wannan Faye mai shekara 44, ya zama shugaban ƙasa mafi ƙarancin shekaru a nahiyar Afirka. Bayan ayyana shi a matsayin wanda ya lashe babban zaɓen ƙasar, Faye ya sha alwashin yin sauye-sauye da dama a ɓangarori daban-daban na ƙasar. An rantsar da Faye ne a ranar Talata a birnin Diamniadio da ke kusa da Dakar babban birnin ƙasar.
Read More
Yunwa ta sanya Falasɗinawa fara cin wata ciyawa a matsayin abinci

Yunwa ta sanya Falasɗinawa fara cin wata ciyawa a matsayin abinci

Sakamakon ƙarancin abinci da kuma barazanar ɓarkewar yunwar ga al'ummar Falasɗinawa, hakan ya tilasta wa wasu da dama dafa ganyen wani haki da suke kira da Khubaiza, don ci a matsayin abinci. Wani magidanci Mohammad Shehadeh ya ce, ya na yin kasada da rayuwarsa ne wajen ɗebo ganyen don ciyar da iyalansa da kuma sayarwa a kasuwa. Ita ma Maryam Al-Attar da ta ce sojojin Isra'ila sun tava harbin su ita da mai gidanta a lokacin da su ka je ɗebo ciyawar ta Khubaiza a gabashin Gaza, ta ce lokacin da ƙananan 'ya'yanta suka ce mata suna jin yunwa, hankalinta…
Read More
Ɗan shekara 44, Bassirou ya lashe zaɓen Senegal

Ɗan shekara 44, Bassirou ya lashe zaɓen Senegal

Shugaba Sall ya taya Bassirou murnar lashe zaɓe Daga BASHIR ISAH Bassirou Diomaye Faye ɗan shekara 44, ya zama sabon zaɓaɓɓen Shugaban Ƙasar Senegal bayan da ya lashe zaɓen shugaban ƙasa da ya gudana a ƙasar. Tuni dai Shugaban Ƙasar mai narin gado, Mavky Sall ya taya Bassirou murnar lashe zaɓen. Bayan ayyana shi a matsayin sabon zaɓaɓɓen Shugaban Ƙasar Senegal, Bassirou ya yi wa ‘yan ƙasar bayani game da abubuwan da za su sa ran gani bayan ya karɓi ragamar mulkin ƙasar. Haka nan, ya ce gwamnatinsa za ta yi tafiya ne cike da tsare-tsare masu inganci ba tare…
Read More
Ofishin jakadancin Falasɗinu a Nijeriya ya yi Allah-wadai da kisan da Isara’ila ke yi wa Falasɗinawa

Ofishin jakadancin Falasɗinu a Nijeriya ya yi Allah-wadai da kisan da Isara’ila ke yi wa Falasɗinawa

*Ya nuna alhini kan sace ɗaliba a arewacin Nijeriya Daga BASHIR ISAH Ofishin Jakadancin Falasɗinu a Nijeriya ƙarƙashin Abdullah M. Abu Shawesh, ya tir da irin kisan kiyashin da Isra'ila ke yi wa Falasɗinawa. Cikin sanarwar da ya fitar a ranar Juma'a, ofishin ya fara bayani ne da nuna alhininsa kan ɗaliban da aka sace da sauransu a yankin Arewa. Abdullah M. Abu Shawesh ya ce, "Jin irin wannan labari yana motsa ni sosai kuma yana ƙara baƙin cikina "A cewar dokar Yahudawa, dole ne a kashe dukkan mazauna Gaza." "Hukumomin Isra'ila sun amince da wannan nau'in tunzura jama'a, kuma…
Read More
Firaministan Haiti ya kama hanyar murabus saboda matsin lambar ‘yan daba

Firaministan Haiti ya kama hanyar murabus saboda matsin lambar ‘yan daba

Firaministan Haiti Ariel Henry ya yada ƙwallon mangoro domin hutawa da ƙuda, wajen miƙa murabus ɗinsa a matsayin shugaban ƙasar da ke yankin Caribbean, bayan cimma matsaya da ƙungiyar ƙasashen yankin a matsayin mafita na warware rikicin siysar ƙasar. Shugaban ƙungiyar ƙasashen yankin Caribbean kuma shugaban ƙasar Guyana Irfaan Ali, wanda ya tabbatar da shirin murabus din Henry, ya yaba da matakin da ya kira wata dama ta kafa kwamitin shugaban ƙasa na riqon ƙwarya wanda zai naɗa firaministan riƙon kwarya. Henry mai shekaru 74 wanda ke riƙe da kujerar firanministan Haiti da ba zaɓen sa aka yi ba tun…
Read More
Birtaniya ta haramta wa likitoci ‘yan Nijeriya masu aiki a ƙasar zuwa da ‘yan uwansu

Birtaniya ta haramta wa likitoci ‘yan Nijeriya masu aiki a ƙasar zuwa da ‘yan uwansu

Daga BASHIR ISAH Ƙasar Birtaniya ta haramta wa ma’aikatan kiwon lafiya a ƙasar zuwa da 'yan uwansu ƙasar. Ofishin cikin gida na Birtaniya ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Litinin. Sanarwar ta ce an ɗauki wannan mataki ne a matsayin ɓangare na ƙoƙarin da Gwamnatin ƙasar ke yi wajen yaƙi da matsalar shiga ƙasar ba bisa ƙa'ida ba. Ta ƙara da cewa a bara kaɗai, jimillar ma'aikata 120,000 ne suka raka ma'aikata 100,000 zuwa Birtaniya. "Masu ba da kulawa a Ingila da ke aiki a matsayin masu tallafawa bakin haure kuwa, za a…
Read More
An ga watan Ramadan a Saudiyya

An ga watan Ramadan a Saudiyya

Daga BASHIR ISAH Kotun Ƙolin Saudiyya ta ce gobe Litinin shi ne zai zama 1 ga watan Ramadan na 1445 biyo bayan ganin jinjirin watan da aka yi da yammacin Lahadi. Da wannan ake sa ran al'ummar musulmin ƙasar su tashi da azumi a ƙasa kamar yadda jaridar Arab News ta rawaito.
Read More
‘Yan daba sun yi wa filin jirgin saman Haiti dirar mikiya

‘Yan daba sun yi wa filin jirgin saman Haiti dirar mikiya

Kwana guda bayan da gungun ‘yan daba suka ɓalle manyan gidajen yari biyu a Haiti, a yau kuma sun farwa babban filin jirgin saman ƙasar da nufin karve iko da shi. Wannan ta sa dole ƙasashen da ke maƙwaftaka da Haiti suka fara ƙarfafa tsaron kan iyakokin su don gudun fantsamar ‘yan dabar zuwa cikin su. Faya-fayan bidiyo sun nuna yadda aka riƙa musayar wuta tsakanin jami’an sojoji da kuma ‘yan dabar sama da 500. Har kawo yanzu filin jirgin saman na The Toussaint Louverture na kulle yayin da aka dakatar da duk wata zirga-zirga. Ko a makon da ya…
Read More