Ra’ayi

Buhari da ziyarar sa a ƙasar Faransa

Buhari da ziyarar sa a ƙasar Faransa

A kwanaki kaɗan da suka gabata, wato ranar 16 ga Mayu, 2021, ne, Shugaban Nijeriya, Muhammadu Buhari, ya buga bulaguro zuwa Birnin Paris, babban birnin Ƙasar Faransa, inda Shugaban ƙasar ta Faransa, Emmanuel Macron, ya karɓi baƙuncin shugabannin ƙasashen Afrika a taron tattaunawa kan jikkatar da aka sha sakamakon ɓarkewar annobar Cutar Korona da kuma duba yiwuwar samun tallafi, musamman bisa irin bashin da ya yi wa ƙasashen na Afrika katutu, sannan kuma ya ke ci gaba da ƙaruwa. Sai dai kuma, a sanarwar da Fadar Shugaban Nijeriya da ke Abuja ta bayar mai ɗauke da sa hannun Babban Mai…
Read More
Wa Zai Auri Ma’aikaciyar Lafiya?

Wa Zai Auri Ma’aikaciyar Lafiya?

Daga AMINA YUSUF ALI Kafin mu shiga cikin bayanin ka'in-da-na'in, ya kamata ma mu sani bangaren da muke magana a kai wato ƙasar Hausa. A ƙasar Hausa da ma karatun boko ko aikin mata wani abu ne wanda har yanzu bai samu karɓuwa da hannu bi-biyu ba. Gara ma ga yara maza wasu masu ɗan sassaucin ra'ayin sun rungume shi. Amma ita mace kullum ana ganin ma kamar wani yahudanci ne ko kuma fin ƙarfin miji ne ko iyaye idan ta yi zuzzurfan ilimin boko. Har ma ta fara aiki a ma'aikatar gwamnati ko ma'aikata mai zaman kanta. Kamar aikin…
Read More
Zarcewa da ayyukan alheri har bayan Ramadan

Zarcewa da ayyukan alheri har bayan Ramadan

Kamar yau aka fara azumin watan Ramadana ranar 13 ga Afrilu, 2021, wanda ya zo daidai da 1 ga Ramadan, 1442, ga shi a shekaranjiya Laraba, 13 ga Mayu, 2021, wanda ya zo daidai da 30 ga Ramadan, 1442, an kammala azumin, kuma a jiya Alhamis aka gudanar da Sallah Ƙarama, wato ranar 1 ga Shawwal, 1442, kenan. Wannan ya gwada irin izinar da rayuwa ke da ita ta cewa, kullum ran mutum yana ƙarewa cikin hanzari ne. A lokacin da muke yi muku maraba da shigowar watan azumin Ramadana mai taken ‘Yayin da watan Azumi ya }arato’, a shafin…
Read More
Za a iya sace kowa a Arewa?

Za a iya sace kowa a Arewa?

Daga NASIRU ADAMU EL-HIKAYA Ba mamaki a iya sace kowa musamman in dai mutum na yawo a sassan arewacin Nijeriya da dare ne ko ma da rana tsaka. Wannan lamari na satar mutane don neman kuɗin fansa ta zama babbar masana'antar samun kuɗaɗe ga miyagun irin daji dama watakila wasu a cikin gari. Wata dabara ma da matafiya tsakanin Abuja da Kaduna ke yi ita ce bin jirgin ƙasa don kauce wa gamuwa da ɓarayin a titi a yankin nan na Rijana. Wannan dabarar ma akwai lokacin da ba ta ɓullewa don akwai labarin an sace mutane bayan sun sauka…
Read More
‘Yancin Zaɓi

‘Yancin Zaɓi

Daga AMINA HASSAN ABDULSALAM Kwanaki na haɗu da wata uwa wace ɗanta ya sami gurbin karatun injiniya a jami’a, bayan ya biya kuɗin na gani na karɓa, wato acceptance fee sai aka ce masa ai ya yi kuskuren haɗin gambiza a jarabawar samin gurbin karatun jami’a wato jamb ko UME ɗin sa don haka an janye gurbin karatu da aka ba shi. Iyayen yaron ganin yadda yake da ƙwazo suka yi duk yadda za su yi yaron ya karanta abinda ransa ke muradi abin ya faskara, a ƙarshen sai wani kwas ɗin aka ba shi wanda bai kai na injiyan…
Read More
Adawa da siyasantar da matsalar tsaro ba za ta fisshe mu ba

Adawa da siyasantar da matsalar tsaro ba za ta fisshe mu ba

A wannan yanayi da mu ke ciki yanzu na taɓarɓarewar tsaro a sassab Nijeriya, jam'iyyun adawa, ƙungiyoyi masu zaman kansu da 'yan ba-ni-na-iya da kuma masu sharhi akan al'amuran yau da kullum a Nijeriya sun taso gwamnati gaba wajen sukar lamirin ta dangane da abinda ya shafi tsaron ƙasar. Yayin da wasu suke kalaman tunzurawa da ɓatanci tare da nuna siyasa ƙarara a cikin kalaman waɗansu. Wanda hakan yake ƙara rura wutar ƙiyayya tsakanin talaka da masu mulkin, talakawa ba sa ganin ƙoƙarin da gwamnati ke yi, har ta kai ga wasu na tunanin yi mata bore. Wasu kuwa suna…
Read More
Mafita: Me ya sa soyayya take mutuwa bayan aure?

Mafita: Me ya sa soyayya take mutuwa bayan aure?

Daga AMINA YUSUF ALI A makon da ya gabata ne muka zo muku da bayani a wannan jaridar taku ta Manhaja mai farin jini a game da dalilan da suke sanyawa soyayya ta mutu murus bayan aure. A waccan fitowar mun zano dalilai da yawa da sukan sa hakan ta faru. Wannan ya sa wasu makaranta da dama suka yi ta tururuwar kiran waya inda suke ƙorafin cewa an kawo musu cuta amma ba a samar musu da waraka ba. Shi ne ni kuma na yi linƙaya a kogin zamantakewa na tsamo muku wasu daga cikin hanyoyin da za su…
Read More
Taya murna ga gwarzon mawallafi: Mohammed Idris ya cika shekara 55, Blueprint ta cika 10

Taya murna ga gwarzon mawallafi: Mohammed Idris ya cika shekara 55, Blueprint ta cika 10

Daga IBRAHIM SHEME A rayuwa ta, akwai wasu mutum uku da nake kira ‘Chairman’, kuma dukkan su na da alaƙa fiye da guda da junan su. Da farko, su ukun nan daga Jihar Neja suka fito. Biyu daga cikin su ƙabilar Nupe ne, wato dai “Bayin Katsina” kenan. Amma batu na gaskiya, su ukun iyaye na ne. Ko me ya sa haka? Saboda sun taɓa ba ni aiki ko makamancin haka, wannan shi ne abu na biyu. Sai na uku, mutum biyu daka cikin su kowanne na ɗauke da muƙamin Kakakin Nupe, wanda Mai Martaba Etsu Nupe, Alhaji Yahaya Abubakar…
Read More
Me ya sa soyayya ke mutuwa bayan Aure?

Me ya sa soyayya ke mutuwa bayan Aure?

Daga AMINA YUSUF ALI Kamar yadda muka sani ko muke iya gani, yawancin aurarrakin yanzu ana dasa su ne bisa soyayya. Wannan abu haka yake musamman a al'ummar Hausa. Da shuɗewar zamani da ilimi har ma da wayewa sun sa an kusa ma a manta a ana auren dole. Amma abu mafi mamaki shi ne, bayan an yi auren soyayyar wacce kamar a haɗiye juna. Sai kuma wasu abubuwa na rashin jituwa su vullo, a rasa ma gane kan zaman nasu. A haka idan ba a kai zuciya nesa ba, sai rabuwa. Ko kuma idan ba a rabun ba, a…
Read More
Ina mafita ga matsalolin Arewa?

Ina mafita ga matsalolin Arewa?

Daga AMINU ƊANKADUNA AMANAWA Arewa yanki ne daga cikin yankunan dake akwai a dunkulalliyar kasa da turawan mulkin mallaka suka hade yankunan kudu da Arewa waje daya da yanzu muke a ciki da kuma tinkaho da ita ta Nijeriya. Duk da yake ko a arewar ta kasu a yankuna daban-daban, kama daga arewa maso gabas, yamma, dama tsakkiya, yankin na fuskantar kalubalai da tarin matsalolin dake kokarin mayar da yankin saniyar ware. Matsalolin da suka tashi daga talauci da kusan ke akwai a lunguna da sako na jihohi, zuwa na tsaro da ya zama ruwan dare, garkuwa da mutane domin…
Read More