Ra’ayi

Yadda za mu inganta sana’armu don yaƙi da talauci

Yadda za mu inganta sana’armu don yaƙi da talauci

Tare da ABBA ABUBAKAR YAKUBU Kamar da wasa aka fara sanya hotunan kayan sayarwa da sana'o'i a zaurukan sada zumunta, ana aikawa da wanda aka saya, bayan an biya kuɗin ta banki, a motocin haya ko ta hannun wasu amintattu, yanzu wannan hanyar tallata kasuwanci ta zama babbar harka da miliyoyin ’yan kasuwa maza da mata ke samun kuɗaɗe masu yawa da abin rufin asiri. Da dama daga cikin waɗanda suke wannan kasuwanci ko dillanci, basu da rumfa ko shago, a gida suke ajiye kayansu, sai an saya sannan su fitar da shi zuwa tasha. Wasu kuwa ma ba su…
Read More
Muhimmancin taimako

Muhimmancin taimako

Assalamu alaikum! Godiya ga Allah Maɗaukakin sarki, da ya sake ba ni damar aika wasiƙa ta zuwa ga al’umma, ta wannna jarida (Blueprint Manhaja) mai albarka. A matsayinmu na mutane masu hankali, abu ne da ya kamata kowa ya gane cewa, duk wani ɗan Adam, komai muqaminsa, komai ƙarfin arzikinsa, komai ƙarfin jikinsa, yana buƙatar taimako. Idan ba ya buƙatar tallafin dukiya, to yana buƙatar wani, idan bai buƙatar wani tallafin, to ala tilas ɗinsa, yana da wata buƙatar daga ɗan uwansa mutum. Kamar yadda al’amarin yake, Allah Ya halicci ɗan Adam ne a matsayin mai kasawa, wanda dole ne…
Read More
Siyasar talaka

Siyasar talaka

Tabbas talakawa ne a gidan gaba wajen yin sanadin samun nasara ga duk wani wanda ya fito takara. Talaka ne wanda zai yi siyasa ta a mutu a kan wani ko a kan jam'iyya amma kuma duk da hakan a yi nasara ya zamo an juya mai baya an dafe madafun iko. Tabbas an daɗe a nai ma talakawa alƙawura kamar da gaske wanda idan nasara ta zo sai dai su bar ma Allah haƙƙin su. Ina fatan yan siyasa su riqa kyakkyawar kula cewa ba ka zamaninka kuma kai na wasu idan ma an zave ka ko kuma an…
Read More
Makamashi: Matatun man fetur a ƙasa

Makamashi: Matatun man fetur a ƙasa

Tare da BASHIR MUDI YAKASAI A kullum manazarta da masana al’amuran yau da kullum za ka ji hikimomi a lafuzansu, kamar da suke cewa, “mai uwa a gindin murhu…”, suka ce, “ba zai ci tuwansa gaya ba,” wato ba miya. Amma abin takaici a Nijeriya da muke da rijiyoyin man fetur sama da 100 da suke fitar da ɗanyen man fetur fiye da ganga milliyan biyu a kullum, amma matatun man fetur na ƙasa ba sa aiki sama da shekaru 10, kuma babu wani dalili tartibun na rashin aikin nasu. Idan muka bi tarihin kakkafa matatun makamashin man fetur da…
Read More
Jihohin Arewacin Nijeriya suna fuskantar masifar yunwa

Jihohin Arewacin Nijeriya suna fuskantar masifar yunwa

Jihohin Katsina, Zamfara, Borno, Kano, Kaduna, Yobe, Nasarawa da Katsina kusan mutane miliyan 20 suna fuskantar qarancin abinci saboda janye tallafin mai da gwamnatin da ta gabata ta assasa sabuwar gwamnatin Tinubu kuma ta aiwatar. Lamarin ya sa mutane ba sa iya sayen abinci su ci saboda matsanancin talauci da rashin tsaro ya haifar. Dokta Abubakar Sulaiman mataimakin shugaban hukumar samar da abinci da bunƙasa noma na Majalisar Ɗinkin duniya shi ne ya bayyana haka cikin hirarsa da BBC. Inda ya ce, janye tallafin mai ya sa matuƙar ana son mutane su rayu dole a ba su kuɗin sayen abinci…
Read More
Matsalar matsananciyar yunwa a Nijeriya

Matsalar matsananciyar yunwa a Nijeriya

An yi hasashen cewa 'yan Nijeriya miliyan 25 na iya fuskantar matsananciyar yunwa tsakanin watan Yuni zuwa Disambar 2023 idan ba a ɗauki matakan gaggawa ba don magance matsalar. Asusun Kula da Ƙananan Yara na Majalisar Ɗinkin Duniya (UNICEF) ya nakalto Cadre Harmonise a watan Oktoba na shekarar 2022, wani bincike na abinci mai gina jiki ƙarƙashin jagorancin gwamnati da Majalisar Ɗinkin Duniya, yana mai nuni da cewa an yi hasashen cewa alƙaluman na ƙaruwa daga sama da mutane miliyan 17 da ke fuskantar barazanar ƙarancin abinci a halin yanzu a ƙasar. A cikin wannan adadi, mutane miliyan uku suna…
Read More
Bayan tsaftace ƙasa daga fasadi sai a waiwayi yunwa

Bayan tsaftace ƙasa daga fasadi sai a waiwayi yunwa

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU A lokacin da nake wannan rubutun, jami'an Hukumar Hisba ta Jihar Kano na can na aikin tantance matasan da jami'anta suka kama bisa laifin aikata fasadi, yawon dare, da mu'amala a wuraren da suke ɓata tarbiyyar al’umma, biyo bayan samame da suke kai wa a wasu gidajen karuwai, kulob-kulob, da ɓoyayyun wuraren da ɓatagari ke fakewa suna aikata ɓarna cikin dare a sassa daban-daban na cikin birnin Kano. Sannan a wata tattaunawa da tashar rediyon Freedom ta yi da wasu daga cikin waɗannan matasa sun bayyana wuraren da aka kama su, da abubuwan da suka ce…
Read More
Kawo ƙarshen matsalar fyaɗe a Nijeriya

Kawo ƙarshen matsalar fyaɗe a Nijeriya

A kwanakin baya ne alqalin kotun da ke shari’ar laifukan fyaɗe da cin zarafin cikin gida da ke Ikeja, ya yanke wa daraktan kula da lafiya na gidauniyar kula da cutar daji, Dokta Olufemi Olaleye, hukuncin ɗaurin rai-da-rai kan laifin yi wa ’yar uwar matarsa fyaɗe. An tuhumi Olaleye da laifuka biyu na lalata da kuma keta haddin ’yar uwar matarsa, laifukan da ake zarginsa da aikata tsakanin Maris 2020 da Nuwamba 2021. An gurfanar da wanda ake tuhuma a ranar 30 ga Nuwamba, 2022 kuma ya musanta aikata laifin. Kwana ɗaya da faruwar, kotun da ke zamanta a Legas,…
Read More
Kotun Allah ya isa: Tsakanin Allah ya isa da Allah ya yi albarka

Kotun Allah ya isa: Tsakanin Allah ya isa da Allah ya yi albarka

Tare da NASIRU ADAMU EL-HIKAYA Fassara ce ta Hausawa ko a ce kirari da a ke yi wa Kotun Qoli cewa “KOTUN ALLAH YA ISA” bisa ma’ana duk hukuncin da ta yanke sai dai a yi haƙuri wanda bai gamsu su ba ya ja Allah ya isa ko ya bar wa Allah wanda shi ne babban mai hukunci ga dukkan talikai kuma ya na ba wa wanda ya so matsayi ya kuma sauke wanda ya iso. Kazalika wanda ya gamsu da hukunci ya kan iya yi wa kotun kirrai a lokacin da kotun “ALLAH YA YI ALBARKA” don shari’a ta…
Read More
Rayuwar ‘yan matan Arewa a Tiktok

Rayuwar ‘yan matan Arewa a Tiktok

Tare da ABBA ABUBAKAR YAKUBU Na daɗe ina son na yi wannan rubutun domin jan hankali da faɗakarwa ga al'ummarmu ta Arewa musamman iyaye da ’yan mata game da wasu abubuwa da ke faruwa, amma wasu dalilai suna sa ina jinkirtawa, sai a wannan karon da batun wata yarinya mai suna Rahama Sa'idu da ta yi karatu a Kwalejin Koyar da Aikin Jinya ta Jihar Kebbi ya taso, inda rahotanni ke cewa wai hukumar gudanarwar makarantar ta kore ta saboda rashin mayar da kai a karatu da sharholiyar da aka ce tana yi a manhajar Tiktok. Kodayake wata majiya ta…
Read More