Ra’ayi

Ƙin samar da rigakafin cutar zazzaɓin cizon sauro

Ƙin samar da rigakafin cutar zazzaɓin cizon sauro

Daga NAJEEB MAIGATARI Kwanakin baya tattaunawa ta haɗa ni da wani aboki na, sai yake ce mun ai ana sane aka ƙi samar da rigakafin cutar zazzaɓin cizon sauro (Malaria) duk da irin yanda kuwa cutar ta addabi musamman ƙananun yara da yanda ta ke kashe su. Har ya jefo mun wata tambaya; me yasa ba a damu da samar da rigakafin ‘Malaria’ ba, amma aka damu mutane da yi mu su rigakafin cutar shan inna (Poliomyelitis) duk da cewar yanzu ba a fama da ita? Maganar gaskiya shi ne a wancan lokacin ba ni da amsar tambayar shi, saboda…
Read More
Muzguna wa Mahdi Shehu barazana ne ga yaƙin da Buhari ke yi na daƙile cin hanci

Muzguna wa Mahdi Shehu barazana ne ga yaƙin da Buhari ke yi na daƙile cin hanci

Daga ALIYU ADAMU TSIGA Cutar da Gwamnatin Jihar Katsina ke yi wa wani mai fallasa bayanan sirri, Mahdi Shehu, na yin barazanar yaƙi da cin hanci da rashawa na Shugaba Muhammadu Buhari, a cewar wata ƙungiyar farar hula. Ƙungiyar 'Movement for Good Governance and Greater Nigeria' (MGGGN), gamayyar ƙungiyoyin fararen hula da ke ƙoƙarin ganin bayan cin hanci da rashawa da samar da shugabanci na gari a ƙasar, a cikin sanarwar bayan taron da ta fitar a majalisar zartarwa na kasa da ta gudanar a Abuja a karshen mako, ta yi tambaya kan yakin da gwamnati ke yi da cin…
Read More
Kwara: Fahimtar juna game da hijabi

Kwara: Fahimtar juna game da hijabi

Daga IBRAHIM SHEME Sau da yawa, na kan yi mamakin yadda wasu ’yan Nijeriya ba su so a zauna lafiya; kullum ƙoƙari su ke yi su tsokano wata magana da za a dinga tada jijiyar wuya a kan ta. Dubi dai tataɓurzar da ake yi kan batun saka hijabi na ’yan makaranta mata Musulmi a Jihar Kwara. Wasu Kiristoci sun tashi haiqan a kan cewa ba su yarda mata ɗalibai su sanya hijabi su je makaranta ba. Abin da ya fi ba ni mamaki shi ne masu wannan kamfen ɗin ba wai wasu zauna-gari-banza kaxai ba ne, waɗanda za a…
Read More
Tashin gwauron zabo da farashi ke yi

Tashin gwauron zabo da farashi ke yi

Rahoton da Hukumar Ƙididdiga ta Ƙasa (NBS) ta bayar kwanan nan kan alƙaluman farashin kayan masarufi (CPI) abin damuwa ne matuƙa. Rahoton ya ce jadawalin tashin farashi a Nijeriya ya ƙaru da kashi 12.82 cikin ɗari a watan Yuli da ya gabata, kuma ba a taɓa ganin irin wannan tashin ba a cikin watanni 27 tun daga watan Maris na 2018 lokacin da farashi ya yi bala’in tashi da kashi 13.34 cikin ɗari. Wannan yanayin zai ƙara tavarɓarar da fatara da yunwa da ake ciki, wanda hakan kuma bazarana ce ga Shirye-shiryen Agajin Jama’a (SIPs) waɗanda Gwamnatin Tarayya ke aiwatarwa,…
Read More
’Yan bindiga: A yafe ko a bindige?

’Yan bindiga: A yafe ko a bindige?

Daga IBRAHIM SHEME Kwanan nan Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir Ahmad El-Rufa’i, ya jawo wata muhawara a kan batun a yafe wa ‘yan bindiga ko a kashe su idan an gan su. Matsayar sa ita ce kada a yi wani zaman tattaunawa da su don a samu hanyar da za a warware ibtila’in kashe-kashe da ke faruwa a yankin Arewa-maso-yamma na ƙasar nan. Gara a nuna masu ƙarfin soja, a murƙushe su, babu sassautawa ko jinƙai. A wata hira da aka yi da shi a gidan rediyon BBC, El-Rufa’i ya bayyana cewa duk wata hanyar lalama da za a bi…
Read More
Mawuyacin halin da Fulani makiyaya su ke ciki laifin gwamnonin Arewa ne?

Mawuyacin halin da Fulani makiyaya su ke ciki laifin gwamnonin Arewa ne?

Daga TIJJANI SARKI  A 'yan makonnin nan an sami tashin tashina a wanin ɓangare na jihohin kudancin ƙasar nan, har inda wani gwamna ya ke ba da sanarwar korar ƙabilar Fulani makiyaya daga faɗin jihar sa, abin har ya kai da ƙona musu gidaje da masallaci  duk dai bisa dogaro da su ba 'yan jihar ba ne. Kuma suna kawo yamutsi a jihar, kodayake mun jiyo Gwamnan Jihar Ogun na cewa suna zaman lafiya da Fulani sama da shekaru ɗari a jiharsa. Zai yi kyau mu ɗan yi waiwaye akan ƙabilar Fulani makiyaya wanda suke da ɗumbin yawa musamman a…
Read More
Toshe hanyar abinci a matsayin makami

Toshe hanyar abinci a matsayin makami

Daga IBRAHIM SHEME Toshe wa mutane hanyar da abinci zai isa gare su wani makami ne da ake amfani da shi a lokacin yaƙi. An yi amfani da shi a lokacin Yaƙin Basasar Nijeriya, wato Yaƙin Biyafra. Manufar wannan matakin ita ce a karya lagon abokan gaba, a rage masu ƙarfi, kuma a tilasta masu su aje makaman su. To amma Majalisar Ɗinkin Duniya ta haramta ɗaukar irin wannan matakin a kan farar hula. Duk wanda aka kama ya yi hakan, ya aikata babban laifi; ana iya gurfanar da shi a Kotun Miyagun Ayyuka ta Duniya (ICC). Sashe na  8(2)(b)(xxv)…
Read More
Batun dokar hana hadahada da kuɗin kirifto

Batun dokar hana hadahada da kuɗin kirifto

Kwanan nan ne Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya kaɗa hantar wasu ‘yan Nijeriya lokacin da ya tunatar da bankuna da sauran hukumomin da ke kula da hadahadar kuɗi cewa dokar nan da ta haramta amfani da kuɗin intanet, wato kuɗin kirifto (cryto currency), ta na nan daram. Karo na uku kenan a cikin shekara biyar da babban bankin ya yi magana kan harka da irin wannan kuɗi da ake ganin ta na tattare da babban ganganci a cikin ta. Sakamakon hakan, bankuna sun shiga soke duk wani asusu da aka buɗe da sunan yin harka da irin wannan kuɗin. Majalisar…
Read More
Mafarin matsalar Fulani da yadda za a magance ta (I)

Mafarin matsalar Fulani da yadda za a magance ta (I)

Daga FARFESA UMAR LABDO ShimfiɗaIna yin wannan rubutu a matsayina na Babban Sakataren ƙungiyar FULDAN na ƙasa. FULDAN (Fulani Development Association of Nigeria) ƙungiya ce mai fafutuka don ci gaban Fulani a fagagen ilmi, al'adu, tattalin arziki da zamantakewa. An kafa ta a shekarar 1999, tana da wakilci a yawancin jihohin ƙasar nan kuma tana da alaƙa da ƙungiyoyi takwarorinta a ƙasashe makota. Ƙungiyar tana shirya tarukan wayar da kan Fulani da koya musu sana'o'i da sabbin dabarun kiwo don inganta sana'arsu. Haka nan tana gudanar da azuzuwan yaƙi da jahilci da koyon addini a rugage da ƙauyukan Fulani. GabatarwaAl'ummar…
Read More
Yaƙin Badar tsakanin Buba Marwa da ’yan ƙwaya

Yaƙin Badar tsakanin Buba Marwa da ’yan ƙwaya

Daga IBRAHIM SHEME A ranar Litinin da ta gabata, sabon shugaban Hukumar Yaƙi da Safara da Shan Muggan Ƙwayoyi (NDLEA), Janar Mohammed Buba Marwa (ritaya), ya yi wata magana wadda ya kamata ta farkar da duk ɗan Nijeriya game da matsalar da fataucin muggan ƙwayoyi ke janyo wa ƙasar nan. Cewa ya yi kashi 90 cikin ɗari na muggan laifukan da ake aikatawa a Nijeriya, sakamakon ɗirkar muggan ƙwayoyi da wasun mu ke yi ne. A cewar sa, laifuka irin su hare-haren ‘yan bindiga, ta’adda, satar mutane, fyaɗe da sauran su duk ‘yan ƙwaya ne ke aikata su. Marwa, wanda…
Read More