24
Jul
A kwanakin baya ne Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya umarci jami’an tsaro da su gaggauta gurfanar da waɗanda suka aikata kisan gilla a wasu sassan jihohin Filato da Binuwai. Shugaban ya kuma bayyana tashe-tashen hankula a jihohin biyu a matsayin abin takaici. Baya ga haka, ya kamata jami’an tsaro su dakatar da tashe-tashen hankula a yankin Arewa maso Yamma da Kudu maso Gabas da sauran sassan ƙasar nan. Mummunan hare-haren da aka kai a Jihohin Filato da Binuwai sun haddasa asarar rayuka da lalata gidaje. Tun a ranar 15 ga watan Mayu ne aka fara zubar da jini a…