Addini

HOTUNA: Yadda alhazai suka kwana a Muzdalifa

HOTUNA: Yadda alhazai suka kwana a Muzdalifa

Daga MU'AZU HARƊAWA a Saudiyya Bayan kammala tsayuwar Arfah a ranar Juma'a, mahajjata sun dunguma zuwa Muzdalifa inda suka kwana kamar yadda ibadar aikin Hajji ta tanadar. Bayan sallar Asuba ta yau Asabar, sai suka tafi jifar Jamrah daga nan kuma su zarce zuwa masallacin Harami a Makka su yi Ɗawafi da Sa'ayi sannan su koma Muna su jira kwanaki biyu na jifa ta biyu da ta uku da kuma yin hadaya da sauran su.
Read More
Hajji 2022: Malamai na ci gaba da ilimantar da mahajjatan Najeriya a Saudiyya

Hajji 2022: Malamai na ci gaba da ilimantar da mahajjatan Najeriya a Saudiyya

Daga MU'AZU HARDAWA a Madina A ci gaba da ƙoƙarin ilimantar da mahajjata game da muhimmancin aikin Hajji kaɓaɓɓiya da take yi, Hukumar Hajji ta Najeriya (NAHCON) ta gargaɗi mahajjatan ƙasar da suka isa ƙasa mai tsarki don sauke farali kan su kasance masu lura da kuma bin doka yayin zamansu a Saudiyya. Babban limamin Hukumar 'Yan Sandan Najeriya, Sheikh Alhassan Yaakub, shi ne ya yi wannan gargaɗi a lokacin da yake gabatar da nasiha ga mahajjatan a birnin Madina. Malamin ya buƙaci alhazan su gode wa Allah bisa baiwar da Ya yi musu ta zama daga masu sauke faralin…
Read More
Zul-Hajj: An hori al’umma su dage da aikata alheri

Zul-Hajj: An hori al’umma su dage da aikata alheri

Daga MUAZU HARDAWA a Madina Yayin da aka shiga watan Zul-Hijja, wata na ƙarshe a kalanadar Musulunci, an hori al'umma musamman Musulmi, da su kara himma wajen aikata ibada da sauran ayyukan alheri. Limamin masallacin Manzon Allah (S.A.W) da ke birnin Madina a ƙasar Saudiyya, shi ne ya yi wannan horo sa'inlin da yake gabatar da huɗubar Sallar Juma'a a ranar Juma'ar da ta gabata. Huɗubar mai tsawon minti 30, ta maida hankali ne kan muhimmancin aikin Hajji da Umrah da kuma yin jihadi don daukaka kalmar Allah. Limamin ya ce, dukkan nasara na daga wajen Ubangiji, don haka ya…
Read More
Ku nemi watan Zul-Hijja yau Laraba, cewar Sarkin Musulmi ga al’ummar Musulmi

Ku nemi watan Zul-Hijja yau Laraba, cewar Sarkin Musulmi ga al’ummar Musulmi

Daga AMINU AMANAWA a Sakkwato Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Muhammad Sa'ad Abubakar, ya buƙaci al'ummar musulmi da su soma duban sabon jinjirin watan Zul-hajj daga yau Laraba, 29 ga Yuli daidai da 29, Zul-ƙida, 1443 bayan Hijra. A bayanin da shugaban kwamitin bayar da shawarwari kan lamurran addini a majalisar, Farfesa Sambo Wali Junaidu ya fitar, ya bayyana cewa za a iya kai rahoton ganin sabon jinjirin watan ga hakimi ko uban ƙasa domin isarwa ga majalisar Sarkin Musulmin. Watan Zul-Hajj shi ne wata na 12 daga jerin watannin kalandar Musulunci, wanda a cikin sa ne al'ummar Musulmi kan gudanar…
Read More
Idin Ƙaramar Sallah: Dalilinmu na bijire wa Sarkin Musulmi, cewar Sheikh Lukwa

Idin Ƙaramar Sallah: Dalilinmu na bijire wa Sarkin Musulmi, cewar Sheikh Lukwa

Daga BAKURA MOHAMMAD a Bauchi Sheikh Musa Lukwa, Malamin addinin Musuluncin nan wanda ya jagoranci almajiran sa suka yi Sallar Eid-el fitr a ranar Lahadi maimakon Litinin kamar yadda Sarkin Musulmi ya umarta, ya yi kariya wa wannan manufa tasa. Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammadu Sa’ad Abubakar, wanda shine jagoran ɗaukacin dukkan Musulmin ƙasar nan dai, ya ayyana ranar Litinin da ta gabata ta kasance ranar Eid-ul Fitr. Sarkin Musulmi ya bayyana cewar, ba a bayar da labarin kamawar watan Shawwal, Shekaru 1443 Bayan Hijira ba a ranar Asabar, kuma bisa tabbacin za a tsinkayi watan a ranar Lahadi…
Read More
Ba a ga watan Shawwal ba

Ba a ga watan Shawwal ba

Daga BASHIR ISAH Kwamitin ganin wata na fadar mai alfarma Sarkin Musulmi ya bayyana cewar, ba a samu bayanin ganin jinjirin watan Shawwal ba. Da wannan, ya tabbata bana Azumi 30 za a yi. Tun farko, Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Sa'ad Abubakar III, ya ba da baki kan a nemi jinjirin watan Shawwal a ranar Asabar, 29 ga Ramadana, 1443 wanda ya yi daidai da 30 ga Afrilu, 2022. Ganin watan Shawwal ne zai bai wa Musulmi damar kammala azumin Ramadana sannan a shiga bikin Sallah Ƙarama. Ita ma Saudiyya, ta ba da sanarwar ba ta ga jinjirin watan…
Read More
Bikin Sallah: Gwamnati ta ba da hutun gama-gari na yini 2

Bikin Sallah: Gwamnati ta ba da hutun gama-gari na yini 2

Daga BASHIR ISAH Domin bai wa al'ummar musulmin Nijeriya musamman ma'aikata, damar gudanar da shagulgulan bikin Sallah Ƙarama cikin nishaɗi da annashuwa, Gwamnatin Tarayya ta ba da hutun gama-gari na yini biyu, Litini 2 zuwa Talata 3 ga watan Mayu, 2022. Sanarwar hakan na ƙunshe ne cikin sanarwa da ta fito ta hannun Babban Sakataren Ma'aikatar Harkokin Cikin Gida, Shuaib Belgore a madadin Ministan Harkokin Cikin Gida, Rauf Aregbesola a ranar Alhamis. Ministan ya yaba wa ƙwazo da sadaukarwar da ma'aikatan gwamnati ke nunawa a bakin aiki wanda a cewarsa, hakan ta ƙara wa Nijeriya tagomashi a idon duniya. Sanarwar…
Read More
Ku nemi watan Shawwal ranar Asabra, Sarkin Musulmi ga Musulmin Nijeriya

Ku nemi watan Shawwal ranar Asabra, Sarkin Musulmi ga Musulmin Nijeriya

Daga BASHIR ISAH Mai Alfarma Sarkin Musulmi kuma Shugaban Majalisar Koli na Harkokin Musuluncin Nijeriya, Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar III, ya yi kira ga Musulmin Nijeriya da su nemi jinjirin watan Shawwal a ranar Asabar, 30 ga Afrilu. Sarkin Musulmi ya buƙaci a nemi watan ne biyo bayan shawarar da Kwamitin Neman Wata (NMSC) ya bayar, kamar dai yadda darakta a NSCIA, Arc. Zubairu Haruna Usman-Ugwu, ya bayyana. Basaraken ya ce, duk inda aka samu ganin jinjirin watan Shawwal, a hanzarta a sanar da sarakuna da ‘yan kwamitin duban wata (NMSC) don a sanar da al’umma. A cewar Usman, “Muddin…
Read More
Hajjin 2022: Maniyyaci zai biya kuɗin kujera sama da Naira miliyan biyu da rabi

Hajjin 2022: Maniyyaci zai biya kuɗin kujera sama da Naira miliyan biyu da rabi

Daga BAKURA MUHAMMAD a Bauchi Hukumar Jigilar Alhazai ta Ƙasa (NAHCON) ta ayyana cewar, kuɗin kujerar zuwa aikin hajji na wannan shekara ta 2022 zai haura Naira miliyan biyu da rabi, fiye da ƙarin kashi hamsin 50 cikin ɗari na Naira miliyan ɗaya da rabi da Alhaji ya biya a shekara ta 2019. Bisa wannan sabon tsari, maniyyata waɗanda suka biya kuɗaɗen ajiya wa hukumomin Alhazai na jihohi tun shekarar 2020, a taƙaice za su biya ƙarin fiye da Naira miliyan ɗaya domin samun damar sauke farali a ƙasa mai tsarki. Shugaban hukumar ta NAHCON, Dokta Zikirullah Hassan shine ya…
Read More
Kwana goman ƙarshe na Ramadan

Kwana goman ƙarshe na Ramadan

Daga MARYAM BATOOL Kwanaki goman ƙarshe na wannan wata mai albarka na Ramadan sun kasance wasu muhimmai kuma gwalagwalan ranaku ga dukkan Musulmi. Watan Ramadan wata ne da aka saukar da Alƙur’ani ga Manzon Allah (SAW), wanda ya zamo haske, madogara, garkuwa, arziki da kuma jagora ga musulmai. Manzon Allah (S.A.W) yana cewa; “Duk wanda watan Ramadan ya zo ya wuce ba a gafarta masa zunubansa ba ya zama babban asararre.” A wannan wata ƙofofin aljannah a bude suke sannan an rufe na wuta. Don haka Musulmai suke zage damtse wajen samun rabon wannan watan. An ɗaure sheɗanu, kuma an…
Read More