Da ɗumi-ɗumi: Buhari ya janye haramcin Tiwita a Nijeriya

Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya ɗage takunkunmin da ya ƙaƙaba wa kamfanin Tiwita a Nijeriya bayan cika sharuɗɗan da gwamnati ta gindaya masa.

Hakan na ƙunshe cikin wata sanarwa mai ɗuake da sa hannun shugaban hukumar NITDA bayan sahalewa daga ministan sadarwa, Isah Ali Pantami.

Ana sa ran shafin Tiwita ya soma aiki daga ƙarfe 12 na daren yau Laraba.