Da Ɗumi-Ɗumi: Kotu ta yi watsi da buƙatar belin Yahaya Bello

Daga BELLO A. BABAJI

Mai Shari’a Maryanne ta Babbar Kotun Tarayya ta yi watsi da batun neman belin tsohon Gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello.

Alƙalin ta yi hakan ne saboda a lokacin da aka rubuta takardar belin, tsohon gwamnan ba ya hannun Hukumar EFCC, wadda ita ta maka shi kotu.

A ranar 22 ga Nuwamba ne aka shigar da takardar yayin da aka kai Yahaya Bello ofishin EFCC a ranar 26 ga watan kuma aka gurfanar da shi a ranar 27.

Sauran bayanai za su zo daga baya…..