Dokar zaɓe na cigaba da kaɗa hantar gwamnoni

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja

Ganin rashin amincewa da gyaran sashe na 84 (8) na dokar zaɓe da Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya yi, gwamnonin Nijeriya sun shiga ruɗu a ƙoƙarinsu na ganin sun samar da waɗanda za su gaje su da kuma isar da jihohinsu ga masu son tsayawa takarar shugaban ƙasa.

Rahotanni sun nuna cewa, wasu gwamnonin na ƙorafin rashin halartar zaɓukan fidda gwani savanin a baya. Akwai kuma fargabar cewa gwamnonin na iya rasa ikonsu a kan wakilan jam’iyyu na jihohi, musamman a lokacin zaɓen fidda gwani na shugaban ƙasa.

A halin yang dai ’yan takarar shugaban ƙasa a jam’iyyar APC; da babbar jam’iyyar adawa ta PDP, na tsara sabbin dabaru don jan hankalin ‘yan tsirarun wakilan da za su zaɓi waɗanda za su riƙe madafun iko.

Rashin amincewa da muhimmin gyare-gyaren da majalisar dokokin ƙasar ta miƙa wa shugaba Buhari a ranar 13 ga watan Mayu yana da tasiri da dama.

Hakan na nufin cewa zaɓaɓɓun jami’ai, irin su shugaban ƙasa, gwamnoni, ‘yan majalisa, shugabannin ƙananan hukumomi, ministoci da sauran manyan jiga-jigan ’yan siyasa waɗanda suka kasance manyan wakilai a taron jam’iyya a baya ba za su kasance cikin wakilai a yanzu ba.

Hakan na nufin wakilan wucin gadi da aka zaɓa a taron jam’iyyu a jihohi daban-daban ne kawai za su zaɓi ‘yan takarar shugaban ƙasa.

Rashin halartar wakilai ko manyan wakilai yana nufin wakilai 810 ne kawai za su kasance a zaɓen fidda gwani na shugaban ƙasa na PDP, yayin da na APC ke da wakilai 2,340.

Idan aka yi la’akari da lamarin, yawancin masu neman shugabancin ƙasar, waɗanda ke tunanin ’yan takarar da aka amince da su sun yanke shawarar gwada ƙarfinsu da farin jininsu a zaɓen fidda gwani.

Haka zalika, tsohon ƙaramin ministan ilimi, kuma ɗan takarar shugaban ƙasa a ƙarƙashin jam’iyyar APC, Cif Emeka Nwajiuba, ya bayyana a jiya cewa, shiyyar Kudu maso Gabas ba ta aiki kan wani shiri na haɗin gwiwa ba. Tun da farko dai masu neman shiyyar sun ce za su goyi bayan duk wanda ya samu tikitin tsayawa takara.

Wata majiya ta shaida wa manema labarai cewa, fitowar ɗan takarar shugaban ƙasa na kudu maso yamma a jam’iyyar APC, gabanin zaɓen fidda gwani na ranar 29 ga watan Mayu, ba zai yiwu ba, duk da alƙawarin da shugabannin jam’iyyar na shiyyar suka yi bayan wani taro a Legas, kwanan nan.

Da ya ke magana kan rashin halartar gwamnonin a zaɓen fidda gwani, gwamnan jihar Akwa Ibom kuma ɗan takarar shugaban ƙasa a jam’iyyar PDP, Udom Emmanuel, ya shaida wa manema labarai bayan taron majalisar dokokin jihar da na majalisar wakilai ta PDP a ranar Lahadin da ta gabata, ya ce, ba a tava tunanin lamarin da aka samu ba.

Kalamansa ya ce, “a ranar Lahadi na yanke shawarar bin ƙa’idojin dokar zaɓe da ta hana ni zama wakili. Shi ya sa na ƙasa zuwa kusa da wurin taron. Wato lamba ɗaya.

A halin da ake ciki, Nwajuiba ya bayyana dalilan da suka sa ake samun yawan masu neman takarar shugaban ƙasa daga yankin Kudu maso Gabas da ke neman tsayawa takara a jam’iyyar APC.

Tare da ’yan takara bakwai da suka fito daga Kudu maso Gabas, wasu masu ruwa da tsaki na ganin ya kamata yankin ya yi jerin gwano a bayan mai takara ɗaya domin ƙarfafa buƙatarta gyara ƙasar.

Da ya ke magana a wani taron manema labarai ranar Litinin a Abuja, Nwajiuba, ya ce, yankin Kudu Maso Gabas zai fi jin daɗin samun ƙarin masu neman shiyyar ta yadda ’yan Nijeriya za su samu zaɓin da za su zaɓa.

A ranar Lahadin da ta gabata ne masu neman tikitin takarar Shugaban Ƙasa a shiyyar Kudu maso Gabas a ƙarƙashin jam’iyyar APC suka gana a Abuja inda suka yanke shawarar yin layi a bayan duk wanda ya samu tikitin takarar shugaban ƙasa a jam’iyyar a zaɓen fidda gwanin da za ta yi nan gaba.

Da suka buƙaci a ba da tikitin zuwa yankin, ’gan takarar sun yaba wa ’yan Nijeriya kan goyon bayan da suka bayar da kuma jajircewarsu na ganin an samu shugaban ’yan ƙabilar Ibo a Nijeriya.

Taron wanda Sanata Rochas Okorocha ya jagoranta kuma Dr Ogbonnaya Onu ya jagoranta ya samu halartar wasu mutane biyar da suka yi takara. Sun haɗa da Cif Ikeobasi Mokelu, Sanata Ken Nnamani, Mrs Uju Kennedy Ohanenye, Gwamna Dave Umahi da Nwajiuba.

Sai dai Nwajiuba ya ce, duk da cewa bakwai daga cikin masu neman takarar sun fito ne daga yankin Kudu maso Gabas, amma wakilan jam’iyyar na da isassun zaɓin da za su zaɓa.

Haka zalika, yiwuwar ɗan takara ɗaya ya fito daga yankin Kudu maso Yamma a kan dandalin jam’iyyar APC ba zai yiwu ba.

Wata majiya ta bayyana cewa, hanya ɗaya tilo da ɗan takarar da aka amince da shi zai iya fitowa ita ce idan aka yi takura.

A wani labarin kuma, mataimakin shugaban ƙasa Farfesa Yemi Osinbajo ya bayyana cewa, nan ba da daɗewa ba shugabanni da dattawan yankin Kudu maso Yamma za su cimma matsaya kan samar da ’yan takarar shugaban ƙasa a shiyyar gabanin zaɓen shugaban ƙasa na 2023.

Ya ce, ana cigaba da tuntuɓar juna a kullum kuma yana da kwarin gwiwar cewa yankin na iya cimma matsaya nan ba da jimawa ba kan saɓanin da ke tsakanin ‘yan takarar.

Sai dai wata majiya da ke da masaniyar ayyukan jam’iyyar APC, ta ce, lamarin na qara cigaba da taɓarɓarewa, kuma masu neman shiyyar ba za su janye wa wasu ba.

Majiyar ta ce, “tsakanin ku da ku, gasa ta yi ƙamari. Akwai buƙatar ku yi magana da juna game da yarjejeniyar, kuma masu burin zama shugabanni su gana da wakilai.

“A matsayinka na mai neman takara, kana da ra’ayin yawan wakilan da suka ba ka tabbacin goyon bayan a zaɓen fidda gwani; a wannan lokacin, tsarin yarjejeniya ba zai iya aiki ba. Abin da na karanta na gani ke nan.”

Majiyar ta ci gaba da cewa, sanya duk wani mai son tsayawa takara zai iya shafar dukiyar jam’iyyar, inda ta dage cewa shugabannin jam’iyyar APC ne kawai waɗanda ba su da sha’awa za su iya yin hakan domin a samu daidaito.

Majiyar ta qara da cewa, “hanya ɗaya tilo da yarjejeniya za ta yi aiki a yankin Kudu maso Yamma ita ce idan akwai wani mataki ko kuma idan ka nemi masu neman shugaban qasa su je su yi zaɓe a tsakaninsu. Idan ka ce mai neman ya sauka ga wani, zai yi wahala.

Duk da haka, Babban Lauyan Osinbajo, Kayode Ajulo, ya bayyana kyakkyawan fata game da fitowar ɗan takarar akan lokacin da ya dace.

Ajulo ya ce, “babu wani ɗan takara a cikin kasafin kuɗin da ya kashe da yawa kamar Osinbajo. Ya zuwa yau, yana cikin jihohi 31, ya ratsa ƙasar. A cikin shekaru bakwai da suka gabata, ya sami damar saduwa da kowa da kowa. Idan ba wai wasu na gwada sa’ar su ba, babu yadda za a yi wani ya kada Osinbajo a zaɓe.

“Imaninmu ga Osinbajo ba wai don shi ne Mataimakin Shugaban ƙasa ba, yana tunatar da kowa abin da ake buƙata don gina ƙasar mai nagarta, kuma wannan shi ne ƙa’idar Yarbawa.”

“Cif Segun Osoba ya yi kyakkyawan aiki inda ya tabbatar wa kowa da kowa yayin taron APC na Kudu maso Yamma cewa, zai yi adalci sosai. Komai na iya zama yarjejeniya, yana da mafi kyawun dama fiye da kowane ɗan takara a 2023.”

A nasa ɓangaren, Darakta Janar na yaƙin neman zaɓen shugaban ƙasa na Asiwaju 2023, Sanata Kashim Shettima, ya bayyana Bola Tinubu a matsayin wanda ya fi cancanta kuma ya cancanta ya mulki ka ƙasar nan a tsakanin duk masu son tsayawa takara.

Ya ce, tsohon gwamnan ya sadaukar da ɗimbin gudunmawa tare da bayar da gudunmawa mai tsoka ga cigaba da wanzuwar jam’iyyar tun daga kan kafuwarta har zuwa tsayawarta cikin biyayya.

Ya ce, Tinubu yana da azama da jajircewa wajen yi wa ’yan Nijeriya hidima da kuma kawar da yankin daga ƙangin rashin tsaro da rashin cigaba.