Daga FATUHU MUSTAPHA
Fitaccen malamin Islman nan na Kaduna, Sheikh Ahmad Gumi, ya yi wata ganawar sirri tare da Tsohon Shugaban Ƙasa Olusegun Obasanjo a gidansa da ke Abeokuta babban birnin jihar Ogun, a Lahadin da ta gabata.
Wata majiya ta kusa da taron, ta ce Gumi ya zaɓi ganawa da Chief Obasanjo ne kasancewarsa na mai faɗa a ji a cikin ƙasa kuma wanda al’umma ke girmamawa.
Malamin ya labarta wa Obasanjo ziyarar da ya kai wa Fulani masu fashi a Arewacin ƙasa da zummar gwamnati ta yi wa yanayin kyakkyawar fahimta da kuma yin aiki da shawarwarin da bayar a matsayin hanyar da za a kawo ƙarshen matsalolin tsaron da suka addabi ƙasa a wannan lokaci.
Takardar bayanin da ta sami sa hannun Obasanjo da Gumi a ƙarshen ganawar tasu, ta nuna su biyun sun yi ittifaƙin cewa matsalolin sace-sacen mutane, fashin daji, ta’addanci da sauran manyan laifuka da ake aikatawa su ne suka haifar da rashin tsaro a ƙasa, kuma abu ne da ya shafi ƙasa baki ɗaya.
Sun nuna cewa na daga cikin dalilan da suka haifar da taɓarɓarewar tsaro a Nijeriya rashin karatu da rashin daidaiton tattalin arzikin ƙasa, sai kuma amfani da addini ta hanyar da ba ta dace ba haɗa da ƙabilanci da kuma sha’anin siyasa.