Gwamnan Gombe ya gaza kawo wa Tinubu akwatin zaɓensa

Daga Daga MAHDI M. MUHAMMAD

Gwamnan Jihar Gombe, Muhammad Inuwa Yahaya, ya kasa kawo wa Tinubu akwatinsa zaɓensa, inda ya sha kaye a hannun jam’iyyar PDP.

A sakamakon zaɓen da aka sanar da jama’a da dama, ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar ya samu ƙuri’u 215 inda ya doke ɗan takarar jam’iyyar APC, wanda ya samu ƙuri’u 186 a jam’iyyar.

Da yake bayyana sakamakon zaɓen, jami’in zaɓe (PO) na mazaɓar Yahaya Umar 010 da ke makarantar gwamnati ta Gombe, Misheal Thomas ya bayyana cewa jam’iyyar NNPP ta samu ƙuri’u 10 ne kacal yayin da LP ta samu ƙuri’u huɗu.

Misheal ya kuma bayyana cewa jam’iyyar ADP ta samu ƙuri’u uku. Ya ce, AA kuma ta samu ƙuri’a ɗaya.

Idan dai ba a manta ba, Gwamna Yahaya ya kaɗa ƙuri’arsa ne jim kaɗan da kaɗa ƙuri’ar hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa (INEC) kan abin da ya kira gagarumin shirin da aka ɓullo da shi a zaɓen 2023.

Ya kuma bayyana cewa ya gamsu da yadda zaɓen ya gudana a jihar.