Gwamnatin Kano ta amince da naɗin kwamitin riƙo na ƙungiyar Kano Pillars

Daga IBRAHIM HAMISU, a Kano

Gwamnan Jihar Kano Engr. Abba Kabir Yusuf, ya amince da naɗin kwamitin riƙo na ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Kano Pillars (Sai Masu Gida).

A cewar sanarwar da Babban Sakataren Yaɗa Labaran Gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa ya sanyawa hannu, ta ce, gwamnati ta naɗa shugaban hukumar da mambobi da sakatare da suka haɗa da:

  1. Babangida Little, Shugaba
  2. Garba Umar, Member
  3. Naziru Aminu Abubakar, memba
  4. Bashir Chilla, memba
  5. Ali Nayara Mai Samba, memba
  6. Shuaibu Ibrahim Doguwa, memba
  7. Rabiu Pele, memba
  8. Muhammed Danjuma, memba
  9. Sabo Chokalinka, memba
  10. Abba Haruna (Dala FM), mamba
  11. Engr. Usman Kofar Na’isa
  12. Yakubu Pele, mamba
  13. Comrade Sani Ibrahim Coach, Sakatare.

Sanarwar ta ƙara da cewar, a ranar Talata aka ƙaddamar da hukumar.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *