Shugaban Jam’iyyar APC na Ƙasa, Sanata Abdullahi Adamu, ya ƙaddamar da Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen APC don zaɓen gwamna da zai gudana a Jihar Osun.
An kafa kwamitin ne ƙarkashin jagorancin Gwamna Babajide Sanwo-Olu na Jihar Legas da takwaransa na Jihar Kano, Gwamna Abdullahi Umar Ganduje.
Sai dai, Gwamna Sanwo-Olu bai samu halartar bikin ƙaddamarwar ba sakamakon wani aikin ƙasa da ya ɗauke shi.