HOTUNA: Yadda CP Gumel da tawagarsa suka yi rangadi yayin zaɓen cike giɓi a Kano

Daga RABI’U SANUSI a Kano

Kwamishinan ‘Yan Sandan Jihar Kano mai kula da aikin zaɓe, CP Usaini Mohammed Gumel, tare da sauran haɗakar jami’an tsaro da ke jihar Kano yayin da tawagarsu ke rangadin duba wasu ƙananan hukumomi dan tabbatar da an samu kwanciyar hankali yayin gudanar da zaɓen cike giɓi da ya guda ranar Asaba.

A cikin tawagar akwai Shugaban DSS, Sibul Difens, Hukukar Kiyaye Haɗurra, Sojoji da sauran hukumomin tsaro.

Wuraren da tawagar ta ziyarta sun haɗar da Zangon Marikita a Rimin Kebe a ƙaramar hukumar Ungoggo, sai Kwaciri Gabas Alasawa da ke ƙaramar hukumar Fagge da sauransu.

Ƙarin hotuna: