IPMAN ta bada umarnin ci gaba da sayar da fetur kan N163

Daga FATUHU MUSTAPHA

Ƙungiyar ‘Yan Kasuwar Fetur Masu Zaman Kansu ta Nijeriya (IPMAN), ta ce ba ta samu wata sanarwar ƙarin kuɗin fetur a hukumance ba, don haka ta buƙaci mambobinta da su yi watsi da jita-jitar da ake ta yaɗawa game da ƙarin farashin fetur.

A wata ganawa da ya yi da manema labarai a wannan Juma’ar, shugaban IPMAN reshen jihar Kano, Bashir Dan-Malam, ya bai wa mambobinsu umarnin su ci gaba da saida fetur kan farashin N163 kowace lita.

Yana mai cewa duk lokacin da aka samu ƙarin farashin mai a ƙasa, masu ruwa da tsaki na fannin za su sanar da IPMAN.

Daga nan, Dan-Malam ya buƙaci ‘yan Nijeriya da su kwantar da hankulansu saboda ƙungiyarsu ba ta da niyyar tsawwala wa ‘yan ƙasa.

Ya ce sun tuntuɓi masu faɗa a ji na fannin fetur game da batun ƙarin farashin inda suka shaida musu babu wani abu kamar haka.

A ƙarshe, shugaban ƙungiyar ya jaddada cewa Hukunar Fetur ta Nijeriya (NNPC), na da wadataccen mai da za ta rarraba wa sassan ƙasa wanda a cewarsa babu buƙatar sayen mai a ɓoye.