Daga AISHA ASAS
An saki sunayen ɗalibai su 17 da aka yi garkuwa da su a Jami’ar Greenfield mai nisan kilomaita 34 da ke babbar hanyar Kaduna zuwa Abuja.
Wani ma’akacin jami’ar da ya buƙaci a sakaya sunansa, shi ne ya bayyana sunayen ɗaliban da lamarin ya shafa.
Ma’akacin ya faɗa cewa ɗaya daga cikin masu gadin makarantar ya rasa ransa yayin harin wanda ya auku ranar Talata, 20 ga Afrilun 2021.
Ga dai jerin sunayen ɗaliban da ‘yan bindigar suka sace wanda baki ɗayansu maza ne babu mace ko guda:
1 Abraham Akinje
2 Fortune Alhassan
3 Miracle John
4 Miracle Turman
5 Jesse Jakiri
6 Joseph Davies
7 Abdullahi Yusuf
8 John Yari
9 Michael Samson Ladan
10 Abdulkareem Ibrahim
11 Kabir Hamisu
12 Lemuel Adamu
13 Israel Antonio
14 Israel Musa
15 Nelson David
16 Mariam Nalado
17 Abdulkadir Abubakar
Sai dai ya zuwa haɗa wannan labari Rundunar ‘Yan Sandan Kaduna ba ce komai ba kan wannan batu.