Daga AISHA ASAS
Hukumar Yaƙi da Yaɗuwar Cututtuka ta Ƙasa (NCDC) ta bada sanarwar samun ƙarin mutum 65 da suka harbu da cutar korona cikin sa’o’i 24 a faɗin ƙasa.
NCDC ta ce ƙarin da aka samu ya shafi wasu jihohi su 11 ne ciki har da jihar Lagos-41, Kaduna-6, Kano-3, Rivers-3, Plateau-3 da kuma Akwa Ibom-2.
Sauran su ne; Imo-2 da Oyo-2 da Edo-1 da Bauchi-1 sai kuma jihar Osun mai mutum 1.
A cewar NCDC, jimillar mutanen da aka tabbatar sun harbu da annobar a faɗin ƙasa ya kama 164,488, yayin da mutum
154,441 sun warke, sannan mutum
2,061 sun rasu sakamakon cutar.