Nijeriya da Ghana za su fafata kan tikitin zuwa Kofin Duniya

Hukumar Ƙwallon Ƙafar Nijeriya (NFF) ta bayyana cewa, tawagar ’yan wasan ƙasarta na Super Eagles za su fafata da takwarorinsu na Ƙasar Ghana a wasan neman tikitin zuwa Gasar Cin Kofin Duniya da Ƙasar Ƙatar za ta karɓi baƙunci a filin wasa na MKO Abiola da ke birnin Abuja.

Sanarwar ta NFF ta ce, za a yi wannan karawar ne a ranar 27 ga watan Maris.
A halin yanzu a na dakon sanarwa daga Hukumar Ƙwallon Ƙafar Ghana kan zagayen farko na wasan neman cancantar da za su buga, wanda ake sa ran ya gudana ko dai a ranar 23 ga watan na Maris ko kuma a ranar 24 ga watan.

Baya ga wasan Nijeriya da Ghana, Jaddawalin wasannin neman tikitin halartar Gasar Cin Kofin Duniya da za ta gudana a Ƙatar ya nuna cewa, Masar da Senegal za su sake kece raini a cikin watan Maris, inda kowacce ƙasa za ta yi tattaki zuwa gidan abokiyar hamayyarta.

A sauran wasannin neman tikitin zuwa Gasar ta Cin Kofin Duniya a Ƙatar, Ƙasar Kamaru za ta kara da Ƙasar Aljeriya, sai Mali da Tunisia, sai kuma Jamhuriyar Dimukaraɗiyyar Kongo da za ta fafata da Moroko.