Sin ta yi kira ga Amurka da ƙasashen Yamma su soke takunkuman da suka yi gaban kansu wajen ƙaƙabawa

Daga CMG HAUSA

Ƙasar Sin, ta yi kira ga Amurka da ƙasashen yammacin duniya, su gaggauta soke takunkuman da suka yi gaban kansu wajen ƙaƙabawa, da dakatar da keta haƙƙoƙin jama’a a wasu ƙasashe.

Wakilin na Sin ne ya yi kiran a jiya, yayin zama na 50 na majalisar kare haƙƙin ɗan Adam ta MƊD, a lokacin da yake halartar tattaunawar da aka yi tsakanin wasu masana masu zaman kansu, a ɓangren haƙƙoƙin bil adama da haɗin giwar ƙasashen duniya.

Fassara wa: Fa’iza