Tinubu ya koma masaukin baƙi na tsaro da zama gabanin rantsar da shi

Shugaban Ƙasa mai jiran gado, Bola Ahmed Tinubu, ya koma masaukin baƙi na tsaro da ke yankin Maitama a Abuja, da zama.

Daraktan yaɗa labarai da hulɗa da jama’a na Tinubu, Bayo Onanuga ne ya bayyana hakan ta hanyar wani faifan bidiyo da ya wallafa a shafinsa na Tiwita a ranar Laraba.

A cewar Onanuga, Tinubu da mataimakinsa Kashim Shettima, za su ci gaba da zama a nan masaukin har zuwa lokacin da za a rantsar da su a matsayin Shugaban Ƙasa da Mataimaki a ranar 29 ga Mayu, 2023.

A ranar Litinin Tinubu ya dawo Nijeriya bayan hutun wata guda da ya sha a Turai.

Ga BIDIYON tafiya masaukin: