Daga CMG HAUSA
Shugaban ƙasar Sin Xi Jinping, ya aike da saƙon taya murna ga zababben shugaban ƙasar Kenya William Ruto a yau Laraba.
Cikin saƙon, shugaba Xi ya ce, Sin da Keyan na da daddadiyyar alaƙar abota da haɗin gwiwa a ɓangarori da dama, waɗanda suka haifar da kyawawan sakamako a shekarun baya-bayan nan.
Ya ce yana ba ci gaban hulɗarsu muhimmanci, kuma a shirye yake ya haɗa hannu da shugaba Ruto, wajen ɗaukaka huldar zuwa wani muhimmin matsayi domin moriyar ƙasashen biyu da al’ummominsu.
Mai fassara: Fa’iza Mustapha