Yadda APC za ta cigaba da mulki a 2023 – Sanata Adamu

Daga MAHDI M. MUHAMMAD a Abuja

Sabon shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Sanata Abdullahi Adamu, ya ce, kwamitin ayyuka na ƙasa (NWC) da ke ƙarƙashinsa zai yi aiki dare da rana domin jam’iyyar ta cigaba da riƙe madafun iko a shekarar 2023.

Adamu, wanda ya yi magana a sakatariyar jam’iyyar APC ta ƙasa da ke Abuja, a ranar Laraba, yayin da ya ke karvar takardar miqa mulki daga gwamnan Jihar Yobe kuma shugaban kwamitin tsare-tsare na riqon ƙwarya mai barin gado, Mai Mala Buni, ya ce, shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ba zai amince da gazawa ba.

Sanata Adamu, tsohon gwamnan jihar Nasarawa, ya ce, lashe zaɓen 2023 aiki ne mai matuƙar wahala amma abu ne wanda ba zai gagara ba, ya kuma buƙaci mambobin kwamitin NWC da sauran masu ruwa da tsaki na jam’iyyar da su sanya ruhin aikin haɗin gwiwa wajen cimma burin jam’iyyar.

“Ta yaya za mu ci zaɓen gama gari? Jama’a suna ta magana, to, ai APC ba ta da wani mai mulki a tikitin takara. Zamu sami daraja da mutunci da gadon shugaban ƙasa na yanzu akan tikitin.

“Don haka, gazawa ba za ta zama kaar APC daga yau ba. Za mu yi aiki don samun nasara tare. Na yi muku alqawarin a cikin ruhin jagoranci na gamayya cewa haɗin gwiwa ita ce hanya ɗaya tilo. Ba zan iya bayarwa ni kaɗai ba. Abin da na ke tambaya shine wani abu da ake kira miƙa wuya.

“Dole ne ku kasance masu aminci. Dole ne ku sami ƙungiya ɗaya. Idan kun kawo ɗabi’ar rarraba, za mu magance shi. Wannan ƙasa ta fi kowannenmu girma. Kuma wannan jam’iyya ta fi kowane ɗan jam’iyyar nan girma. Don haka ruhin da na ke jagorantar ƙasar nan ke nan.

“Kuma ana sa ran mu tashi kamar yadda aka ba mu. Wannan shi ne ruhun da za mu yi aiki da shi.”

Tun da farko, Buni ya roƙi Adamu da ya ci gaba da riƙe abubuwan gadon da kwamitin riƙo ya yi.

“A matsayinku na mambobin NWC na jam’iyyar, kuna da aiki mai wuyar gaske. Na farko, don cigaba da samun nasarori da kuma zuwa a daidai lokacin da wannan jam’iyyar za ta fara gabatar da takara. Kuma a fili, aikin da ke gabanku yana da girma,” inji shi.