Daga BASHIR ISAH
‘Yan Majalisar Jihar Zamfara sun zaɓi Honorabul Bilyaminu Isma’il daga Ƙaramar Hukumar Zurmi a matsayin sabon Shugaban Majalisar ba tare da hamayya ba.
Kazalika, sun zaɓi Adamu Aliyu Birnin Magaji daga Ƙaramar Hukumar Gummi a matsayin Mataimakin Shugaban Majalisar.
Sun gudanar da zaɓen ne a ranar Talata a zauren majalisar da ke Gusau, babban birnin jihar.