Daga WAKILINMU
Ana zargin wani matashi da yin garkuwa da mahaifinsa a Jihar Kwara inda ya buƙaci a biya fansar miliyan N2.5.
A sanarwar manema labarai da ya fitar a Ilorin Mai magana da yawun ‘yan sandan jihar, Ajayi Okasanmi, ya ce jami’an rundunar yaki da masu garkuwa da mutane a jihar sun cafke yaron.
“Yayin bincike wanda ake zargin ya yi ikirarin yin garkuwa da mahaifin nasa bayan haɗa baki da wasu mutum biyu.
“Lamarin ya auku ne a yankin Igboho/Igbeti Oyo inda suka karɓi kuɗin fansa N2.5m ransom,” in ji shi.
Jami’in ya ce suna ci gaba da bincike don kamo sauran da ke da hannu a badaƙalar.