Yanzu-yanzu: ‘Yan bindiga sun kashe mutum ɗaya tare da yin garkuwa da fararen hula sama da 10 a Zamfara

Spread the love

Daga SANUSI MUHAMMAD a Gusau

Wasu ‘yan bindiga sun sake kai wani sabon hari a garin Maru ƙaramar hukumar Maru a Zamfara, inda suka kashe wani matashi da akafi sani da Attahiru Abubakar.

Wani mazaunin garin da ya nemi a sakaya sunansa ya shaidawa wakilinmu ta wayar tarho cewa ‘yan bindigar sun mamaye garin ne da misalin karfe 2:00 na daren yau.

Ya ce, ‘yan bindigar sun yi garkuwa da iyalan marigayi Attahiru tare da wasu mutane tara a yayin harin.

Jaridar Blueprint Manhaja ta rawaito cewa ƙaramar hukumar Maru na ɗaya daga cikin ƙananan hukumomin da ‘yan bindiga suka saba kai hari a lokuta da dama.

Wannan mummunan al’amari ya nuna yadda matsalar tsaro ke ta ƙara kunno kai a ƙaramar hukumar.

Cikakken rahoton daga baya zai zo

By ukarofi