ukarofi

11670 Posts
Gwamnatin Zamfara ta gargaɗi malamai da aka horar kan su guji sakaci da aiki

Gwamnatin Zamfara ta gargaɗi malamai da aka horar kan su guji sakaci da aiki

Daga SANUSI MUHAMMAD a Gusau Gwamnatin Jihar Zamfara ta yi gargaɗi ga malaman makarantun sakandare 250 da aka horar kan su guji yin sakaci kan aikin su, tana mai cewa duk wani malami da aka samu yana da halin rashin ɗa'a da rashin zuwa aiki zai fuskanci hukuncin ladabtarwa bisa ga doka. Kwamishinan Ilimi, kimiyya da fasaha, Hon. Abdulmalik Gajam ne ya bayar da gargaɗin a yau Asabar a bikin rufe taron horar da malamai na tsawon makonni biyu na shirin Global Standard Change Program (GSTTP) da aka gudanar a Gusau. Shirin gina ƙarfin aiki ya samu hirar da malaman…
Read More
Sarkin Katsina ya naɗa sabbin hakimai bakwai

Sarkin Katsina ya naɗa sabbin hakimai bakwai

Daga ABDULLAHI MUHAMMAD a Katsina Mai martaba Sarkin Katsina ya naɗa sabbin hakimai bakwai ciki har da tsohon Ministan Sufuri Sanata Hadi Sirika a masarautar Katsina. Naɗin wanda ya gudana a fadar Sarkin Katsina ya zo ne a wani mataki na ƙarfafa tsarin gudanar da harkokin masarauta da kuma inganta shugabanci a yankunan da hakiman ke jagoranta. Hakiman da aka naɗa sun hada da Alhaji Sani Tukur Mu’azu Sarkin Rumah Katsina, Hakimin Batsari da Alhaji Abba Lawal Sani Dutsi Gabasawan Katsina, Hakimin Dutsi. Saura sun haɗa da Alhaji Gambo Abdullahi Dabai Dausayin Katsina, Hakimin Dabai daAlhaji Zakari Maina, Dan Yusufan…
Read More
Mun yi adawa da yunƙurin Atiku na cire tallafin mai a zamanin Obasanjo – Hashim

Mun yi adawa da yunƙurin Atiku na cire tallafin mai a zamanin Obasanjo – Hashim

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD ɗan Takarar Shugabancin ƙasa na Jam’iyyar Accord, Dakta Gbenga Olawepo-Hashim, ya bayyana cewa shugabannin jam’iyyar PDP a zamanin mulkin tsohon Shugaban ƙasa Olusegun Obasanjo sun yi watsi da yunƙurin tsohon Mataimakin Shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, na cire tallafin man fetur. Olawepo-Hashim ya ce ra’ayin Atiku na cire tallafin mai ya samo asali tun kafin gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, yana mai bayyana tsohon mataimakin shugaban ƙasar a matsayin ɗaya daga cikin manyan jiga-jigan farko da suka fara fafutukar ganin an cire tallafin man fetur tare da mayar da kamfanonin gwamnati gaba ɗaya hannun masu zaman kansu…
Read More
’Yan Nijeriya sun zama ja-gaban duba shafukan intanet na batsa, caca da AI a Yulin 2026

’Yan Nijeriya sun zama ja-gaban duba shafukan intanet na batsa, caca da AI a Yulin 2026

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD ’Yan Nijeriya sun kai miliyoyin ziyara ga shafukan intanet da suka shafi abubuwan batsa, wasannin caca da kuma manhajojin ƙirƙirarriyar basira ta AI a watan Yulin 2026, kamar yadda bayanan Semrush Traffic Analytics suka nuna. Bayanan da kamfanin Semrush ya fitar kan shafukan intanet da aka fi ziyarta a Nijeriya a watan Yuli sun nuna cewa Google ne ya kasance kan gaba, inda ya samu ziyara miliyan 318.45. A matsayi na biyu kuwa akwai YouTube, wanda ya samu ziyara miliyan 46.42. Shafin Sɓideos, wanda ke ƙunshe da abubuwan batsa, ya zo na uku da ziyara miliyan…
Read More
Binance ya hana amfani da A7 Nigeria da A7 Africa bayan tsaurara matakan Kirifto

Binance ya hana amfani da A7 Nigeria da A7 Africa bayan tsaurara matakan Kirifto

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Kamfanin musayar kuɗaɗen dijital na Binance ya sanar da wani sabon mataki na tsaurara bin ƙa’idojin hada-hadar kadarorin crypto, inda ya dakatar da mu’amalar kuɗi da wasu dandamali 16, ciki har da A7 Nigeria da A7 Africa, waɗanda ke da alaƙa da masu amfani a Nijeriya. Sabon matakin zai fara aiki ne daga 23 ga Agusta, 2026, yayin da Binance ke ci gaba da aiwatar da takunkumin a matakai daban-daban. Binance ta ce matakin ya shafi wasu masu samar da hidimomin kadarorin crypto, kuma ta shawarci masu amfani da kada su aika ko karɓar kuɗi kai…
Read More
Nijeriya na shirin inganta lantarki don amfanin gida da waje — NISO

Nijeriya na shirin inganta lantarki don amfanin gida da waje — NISO

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Nijeriya ta fara sake tsara harkokin wutar lantarki domin samar da isasshiyar wuta ga masu amfani da ita a cikin ƙasa, tare da samun damar fitar da rarar wutar zuwa kasuwannin ƙasashen Yammacin Afirka, inji Mai Kula da Tsarin Samar da Wutar Lantarki Mai Zaman Kansa na Nijeriya (NISO). Hakan na zuwa ne yayin da Kamfanin Isar da Wutar Lantarki na Nijeriya (TCN) ya bayyana cewa tsarin layukan wutar lantarkin ƙasar a yanzu na da ƙarfin iya jigilar kusan megawatt 8,700 na wuta. Manajan Daraktan NISO, Abdu Mohammed, ya shaida wa manema labarai cewa ana mayar…
Read More
2027: Yadda tsadar allunan talla ya jefa ’yan takara cikin ruɗani

2027: Yadda tsadar allunan talla ya jefa ’yan takara cikin ruɗani

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Yayin da aka fara yaƙin neman zaɓe a hukumance domin zaɓen shugaban ƙasa da na’yan Majalisar Dokoki ta ƙasa, hankula sun karkata kan yadda ’yan takara za su yi amfani da kafafen yaɗa manufofinsu, domin jan hankalin masu zaɓe gabanin babban zaɓen 2027. A halin yanzu, Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta ƙasa (INEC) ta tantance ’yan takarar shugaban ƙasa 19 da za su fafata a zaɓen da aka shirya gudanarwa a watan Janairun 2027. Daga cikin hanyoyin da jam’iyyu da ’yan takara suka saba amfani da su akwai tarukan gangami, shirye-shiryen kai tsaye da na…
Read More
Buratai ya yi gargaɗi kan katsalandan ɗin ƙasashen waje a batun Tinubu

Buratai ya yi gargaɗi kan katsalandan ɗin ƙasashen waje a batun Tinubu

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Tsohon Shugaban Rundunar Sojojin Nijeriya, Laftanar Janar Tukur Buratai (mai ritaya), ya yi kira ga ’yan Nijeriya da su yi tsayuwa tsayin daka wajen kare ikon mulkin ƙasar, tare da yin watsi da duk wani yunƙurin tsoma bakin ƙasashen waje cikin harkokin cikin gida. Kiran na Buratai ya biyo bayan matakin da ake ƙoƙarin ɗauka na fitar da wasu takardu da ake zargin suna da alaƙa da binciken safarar miyagun ƙwayoyi da ya shafi Shugaba Bola Ahmed Tinubu, wanda ake cewa binciken ya samo asali ne tun kimanin shekaru 33 da suka gabata. Sai dai tsohon…
Read More
Sojin sama na Nijeriya sun kashe mayaƙan ISWAP a Borno

Sojin sama na Nijeriya sun kashe mayaƙan ISWAP a Borno

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Rundunar Operation Haɗin Kai (OPHK) ta gudanar da hare-haren sama kan mayakan ƙungiyar ISWAP a ƙauyen Aduwa, ƙaramar hukumar Guzamala ta Jihar Borno. Rahotanni sun ce hare-haren, waɗanda aka kai ranar 21 ga Agusta, 2026, sun hallaka wasu mayakan ISWAP tare da lalata motocin yaƙi guda biyu na ƙungiyar. Zagazola Makama, wata kafar yaɗa bayanan yaƙi da ta’addanci, ta ce bayanan sirri sun nuna cewa hare-haren sun yi tasiri sosai, inda dukkan mutanen da aka gani a wurin da aka kai harin aka tantance su a matsayin mayakan ISWAP. A cewar rahoton, ɗaya daga…
Read More
Ba cire tallafin mai Tinubu ya yi ba, kawai abokan sa ya danƙawa dukiyar ƙasa – Atiku

Ba cire tallafin mai Tinubu ya yi ba, kawai abokan sa ya danƙawa dukiyar ƙasa – Atiku

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, ya zargi gwamnatin Shugaba Bola Tinubu da yin nuƙu-nuƙu kan batun cire tallafin man fetur. Atiku ya ce gwamnati ba za ta ce ta kawo ƙarshen tallafin man fetur ba, alhali tana bai wa masu zuba jari a harkar man fetur rangwamen haraji, tallafin kuɗi da sauran gata na musamman. A cikin wata sanarwa da mai taimaka masa kan harkokin yaɗa labarai, Phrank Shaibu, ya fitar ranar Lahadi, Atiku ya bayyana bikin da gwamnatin Tinubu ke yi kan cire tallafin a matsayin “ɗaya daga cikin manyan yaudarar tattalin…
Read More