ukarofi

11000 Posts
Ɗaukar doka a hannu ke janyo faɗa tsakanin manoma da makiyaya – Alhaji Akote

Ɗaukar doka a hannu ke janyo faɗa tsakanin manoma da makiyaya – Alhaji Akote

Daga JAMIL GULMA a Kebbi Shugaban ƙungiyar Miyetti Allah reshen ƙaramar hukumar Argungu Alhaji Hara Akote Badariya ya bayyana ɗaukar doka a hannu ne dalilin faɗa tsakanin manoma da Fulani makiyaya.Ya yi wannan bayanin ne a wata hira da ya yi da waƙilin jaridar Blueprint Manhaja a garin Argungu.Alhaji Akote Badariya ya ce tsakanin manoma da Fulani a ƙasar nan ba wanda ke iya raba su saboda ɗaya bai yi sai da ɗaya don haka suka tarar tun kakanni da iyaye, idan makiyaya suka yi ɓarna ko dai a yi sulhu tsakanin su ba sai an je ga hukuma ba…
Read More
Dangin juna Afirka ta karrama Danbayo da lambobin yabo biyu kan ayyukan jin ƙai

Dangin juna Afirka ta karrama Danbayo da lambobin yabo biyu kan ayyukan jin ƙai

Daga ABUBAKAR A. BOLARI Gombe Ƙungiyar dangin juna Afirka Initiative (DJAI) ta karrama babban mataimaki na musamman ga Gwamnan Jihar Gombe kan harkokin tsaro da hulɗa da sauran hukumomi, Ambasada Yusuf Musa Danbayo, da lambobin yabo guda biyu saboda ayyukansa na jin ƙai da gudummawar da yake bayarwa wajen ci gaban al'umma. An miƙa lambobin yabon ne a wajen bikin rufe taron ƙasa na DJAI na National Retreat 0.2, wanda aka gudanar a Yankari Game Reserve da ke Jihar Bauchi. Da yake gabatar da lambobin yabon, shugaban ƙungiyar na ƙasa, Usman BK, ya ce an zaɓi Danbayo ne saboda jajircewarsa…
Read More
Hon Safana ya yi alƙawarim ci gaba da farfaɗo da shirin bunƙasa al’umma

Hon Safana ya yi alƙawarim ci gaba da farfaɗo da shirin bunƙasa al’umma

Daga ABDULLAHI MUHAMMAD a katsina Mai bai wa gwamnan Jihar Katsina shawara kan ayyukan ƙananan hukumomi, Hon. Lawal Rufa'i Safana, ya jaddada muhimmancin farfaɗo da shirin Community Development domin ƙarfafa ci gaban al'umma a dukkan ƙananan hukumomin jihar. Hon. Safana ya bayyana hakan ne lokacin da shugabanni da mambobin ƙungiyar daraktocin Ilimi da ci gaban al'umma (ESD) na ƙananan hukumomi suka kai masa ziyarar neman goyon baya a ofishinsa. Ya ce sashen ayyuka zai samar da kayan aikin Community Development domin rabawa ƙananan hukumomi, inda ya bayyana cewa za su kasance ƙarƙashin kulawar sassan ESD. Ya kuma yi bayani kan…
Read More
Kotu ta mayar wa kamfani mallakar fili a Gombe tare da diyyar Naira miliyan 65

Kotu ta mayar wa kamfani mallakar fili a Gombe tare da diyyar Naira miliyan 65

Daga ABUBAKAR A BOLARI Gombe Babbar Kotun Jihar Gombe mai lamba ta tara ta tabbatar da cewa kamfanin Emir General Integrated Ltd ne halastaccen mamallakin wani fili mai faɗin hekta 1.30 da ke kan titin Gombe–Bajoga a ƙaramar hukumar Gombe, tare da bai wa kamfanin diyyar Naira miliyan 65 bayan ta gano cewa an kutsa masa tare da rusa kadarorinsa ba bisa ƙa'ida ba. Mai shari'a Daurabo S. Sikkam ce ta yanke hukuncin a shari'a mai lamba GM/116/2026, inda ta tabbatar da cewa takardar mallakar fili (Certificate of Occupancy) mai lamba GM/15926 da kamfanin ke da ita tana nan da…
Read More
‘Yan sanda sun sami nasarar ceto mata biyu daga hannun ‘yan bindiga a Katsina

‘Yan sanda sun sami nasarar ceto mata biyu daga hannun ‘yan bindiga a Katsina

Daga ABDULLAHI MUHAMMAD a Katsina Rundunar 'yan sanda a Katsina sun nasarar ceto mata biyu daga hannun 'yan bindiga a ƙaramar hukumar Charanchi tare da daƙile yunƙurin satar dabbobi a ƙaramar hukumar Charanchi. Kamar yadda jami'in hulɗa da jama'a na rundunar 'yan sanda a Katsina DSP Abubakar Sadiq Aliyu ya sanar, ofishin 'yan sanda a Kankia suka sami labarin cewa 'yan bindiga a kan baburan hawa ɗauke da muggan makamai sun Kai hari a matsugunin Jauga a ƙauyen Sabon Gida da ke Kankia. Ya bayyana cewa nan take jami'an 'yan sanda suka isa ƙauyen inda su kai ta ɗauki ba…
Read More
‘Yan ta’adda sun kashe jami’an tsaron daji biyu a Kebbi

‘Yan ta’adda sun kashe jami’an tsaron daji biyu a Kebbi

Daga JAMIL GULMA a Kebbi Rahotanni daga ƙaramar hukumar Danko-Wasagu sun bayyana cewa aƙalla jami'an tsaron daji (Forest Guard) biyu sun rasa rayukan su bayan bata-kashi tsakanin su da waɗansu maharada a ke sa ran masu garkuwa da mutane ne da suka kai farmaki a gonakin garin Tudunbichi a garin Wasagu safiyar litinin.Wani mazaunin garin na Wasagu da bai so a bayyana sunan sa ba saboda dalilan tsaro ya bayyana cewa da rana ne maharan suka kai farmakin, bayan sanar da jami'an su kuma cikin lokaci suka kai wa mutanen garin ɗauki inda a ka yi musayar wuta na wani…
Read More
Shan miyagun ƙwayoyi na neman kassara makomar matasan Nijeriya

Shan miyagun ƙwayoyi na neman kassara makomar matasan Nijeriya

A duk lokacin da aka ambaci manyan matsalolin da suke yi wa Nijeriya barazana, mutane kan fi karkata hankali ga rashin tsaro, talauci, rashin aikin yi da hauhawar farashin kayayyaki. Sai dai akwai wata annoba da ke ci gaba da kutsawa cikin al'umma cikin shiru, tana lalata rayuwar dubban matasa, tana rusa iyalai, tana haddasa aikata manyan laifuka, kuma tana kassara makomar ƙasa. Wannan annoba ita ce shan miyagun ƙwayoyi da kuma fataucin su. A yau, shan miyagun ƙwayoyi ya zama wani babban ƙalubale da ya wuce matsalar mutum ɗaya ko iyali ɗaya. Matsala ce da ta shafi lafiyar jama'a,…
Read More
Farashin mai a mizani: Rijiyata ta bada ruwa guga ta hana?

Farashin mai a mizani: Rijiyata ta bada ruwa guga ta hana?

Abin mamaki da takaici ne yadda farashin man fetur ya ragu ƙwarai, amma har yanzu wasu dillalan mai sun ƙi sauke farashinsa. Sun ƙi bin sauyin da ya faru, suna ci gaba da sayar da mai yadda suka ga dama. Abin lura shi ne, idan farashin mai ya tashi, ba sa ɓata lokaci wajen ƙara farashi. Amma idan ya sauka, sai su yi kunnen uwar shegu, kamar ba su san abin da ke faruwa ba. Mu dai addu'armu ita ce Allah Ya hana duk wanda yake son ganin mun shiga ƙunci cimma burinsa. Tashin farashin da aka sha fama da…
Read More
Ko akwai waɗanda ƙasa ba ta cin jikinsu bayan binnewa?

Ko akwai waɗanda ƙasa ba ta cin jikinsu bayan binnewa?

Daga ALI ABUBAKAR SADIK Shin ko akwai waɗanda ƙasa ba ta cin jikinsu bayan binnewa? Tambayar da Shehil Islami Malam Aminu Bello ya jeho kenan. Da farko akwai bukatar a fahimci fadar Allah cikin Suratul Al Rahman cewa; "Dukkan abinda ke kanta (Duniya) mai ƙãrewa ne. Kuma Fuskarar Ubangijinka, Mai girman Jalala da karimci, ita ce take wanzuwa." Wannan aya cike ta ke da kimiyya da tauhidi. A kimiyance babu wata halitta da ta ke dorewa a Doron Duniya, domin Allah ya tsara duniyar yadda komai na cakuduwa da sabuntawa da karewa. Daga kasa aka halicci duk masu Rai Kuma…
Read More
Tashar lantarki ta Lambar Rimi: Daga shekarun tsaiko zuwa hanyar kammala aiki a bayyane

Tashar lantarki ta Lambar Rimi: Daga shekarun tsaiko zuwa hanyar kammala aiki a bayyane

Daga ABUBAKAR TUKUR IBRAHIM Korafe-ƙorafen da ake yi dangane da tashar samar da wutar Iska ta Lambar Rimi abu ne da ya dace. Kowanne ɗan jihar Katsina na son ganin injinan samar da wutar suna aiki tare da ganin an fara isar da wutar lantarki zuwa gidaje, wuraren kasuwanci, masana'antu da al'ummomi. Sai dai kuma, duk da cewa yana da sauƙi a yi bayanin tarihin aikin, yana da muhimmanci a bayyana gaskiyar abubuwan da suka faru a ƙarƙashin jagorancin mai girma Gwamna Malam Dikko Umaru Raɗɗa, PhD, CON, wajen ceto aikin daga shekaru masu yawa na rashin tabbas tare da…
Read More