14
Feb
Ƙungiyar Igbo Women Assembly (IWA), wata ƙungiyar matan Ibo, ta caccaki gwamnatin jihar Legas bisa ƙudirin koyar da yaren Yarbanci kawai a makarantu na gwamnati. Ƙungiyar ta bayyana cewa za ta gurfanar da gwamnatin Babajide Sanwo-Olu a kotu kan wannan mataki. Shugabar ƙungiyar, Nneka Chimezie, ta bayyana hakan yayin taron manema labarai da aka gudanar a Umuahia ranar Alhamis. IWA na da alaƙa da Ohanaeze Ndigbo, babbar ƙungiyar ƙabilar Ibo. Chimezie ta bayyana damuwarta kan wannan doka a birni kamar Legas da ke da ƙabilu daban-daban. “Ya kamata ne a koyar da Hausa, Igbo da Yarbanci a makarantu, ba wai…