ukarofi

3767 Posts
Ƙabilar Ibo ta koka wa gwamnatin Legas kan koyar da yaren Yarabanci kaɗai a makarantu

Ƙabilar Ibo ta koka wa gwamnatin Legas kan koyar da yaren Yarabanci kaɗai a makarantu

Ƙungiyar Igbo Women Assembly (IWA), wata ƙungiyar matan Ibo, ta caccaki gwamnatin jihar Legas bisa ƙudirin koyar da yaren Yarbanci kawai a makarantu na gwamnati. Ƙungiyar ta bayyana cewa za ta gurfanar da gwamnatin Babajide Sanwo-Olu a kotu kan wannan mataki. Shugabar ƙungiyar, Nneka Chimezie, ta bayyana hakan yayin taron manema labarai da aka gudanar a Umuahia ranar Alhamis. IWA na da alaƙa da Ohanaeze Ndigbo, babbar ƙungiyar ƙabilar Ibo. Chimezie ta bayyana damuwarta kan wannan doka a birni kamar Legas da ke da ƙabilu daban-daban. “Ya kamata ne a koyar da Hausa, Igbo da Yarbanci a makarantu, ba wai…
Read More
NECO ta saki sakamakon jarrabawar 2024

NECO ta saki sakamakon jarrabawar 2024

Hukumar shirya jarrabawa ta Ƙasa (NECO) ta sanar da sakin sakamakon jarrabawar kammala sakandire (SSCE External) na shekarar 2024. Shugaban NECO, Farfesa Dantani Wushishi, ne ya bayyana hakan yayin da yake sanar da sakin sakamakon a Minna ranar Juma’a. A cewarsa, ɗalibai 57,114 ne suka samu maki mai kyau a Turanci da Lissafi, wanda ke wakiltar kashi 67.53% na wucewa. Jimillar ɗalibai 86,067 ne suka zauna jarrabawar, inda aka samu raguwar aikata maguɗin jarrabawa. Wushishi ya bayyana cewa an gwada ɗalibai a fannonin darussa 29, inda 83,220 suka rubuta Turanci, yayin da 83,024 suka rubuta Lissafi. A cewarsa, ɗalibai 62,929…
Read More
Tunawa da shekaru 49 da kisan Janar Murtala Ramat Muhammed 

Tunawa da shekaru 49 da kisan Janar Murtala Ramat Muhammed 

Daga TASKAR NASABA A ranar 13 ga Fabrairu, 1976, aka kashe shugaba mulkin soja na Tarayyar Nijeriya, Janar Murtala Ramat Muhammed, a wani yunƙurin aikata juyin mulki da bai yi nasara ba. An kuma kashe direbansa da gwamnan mulkin soja na Jihar Kwara, Kanar Ibrahim Taiwo a lokacin. Yunƙurin juyin mulkin Nijeriya a shekarar 1976, wani yunƙuri ne na juyin mulkin da sojoji suka yi a Nijeriya a ranar 13 ga Fabrairu, 1976, a lokacin da wani ɓangare na hafsoshin sojin ƙasar ƙarƙashin jagorancin Laftanar Kanar Bukar Suka Dimka suka yi yunƙurin kifar da Gwamnatin Janar Murtala Ramat Muhammed (wanda…
Read More
Yadda ƙananan hukumomin Katsina suka raya yankuna karkaka ƙarƙashin Gwamna Raɗɗa

Yadda ƙananan hukumomin Katsina suka raya yankuna karkaka ƙarƙashin Gwamna Raɗɗa

Daga ABDULLAHI MUHAMMAD a Katsina A cikin shekaru uku da suka gabatar, ƙananan hukumomin Jihar Katsina sun yi rawar gani wajen samar ma al'umomi mazauna yankunan karkara romon dimukraɗiyya ababen more rayuwa, kama daga ta hanyar inganta rayuwarsu da samar musu ababen more rayuwa a fannoni daban-daban, kamar kiwon lafiya, ruwan sha, ilimin da bunƙasa fannin noma da kiwo, da gina hanyoyi da magudanan ruwa da samar da wutar lantarkin da sauransu. Samar da waɗannan ayyuka, manyan da ƙananansu, sun taimaka gaya wajen bunƙasa tattalin arzikin yankunan karkara da samar da ayyukan yi da rage fatara da inganta sufiri da…
Read More
Batun samar da tsaro a makarantu

Batun samar da tsaro a makarantu

A kwanakin baya ne dai rahotanni suka ce gwamnatocin jihohi da hukumomin tsaro da ma’aikatu sun yanke shawarar haɗa ƙarfi da ƙarfe domin magance ta’addanci da nufin samar da ingantaccen tsaro a makarantu. Manufar ita ce a motsa masu ruwa da tsaki don ba da gudunmawa ga shirin, don samar da kuɗaɗe da samar da ingantaccen ilimi a Nijeriya. Baya ga samar da tsaro a makarantu ga yara, haka kuma don a rage yawan yaran da ba sa zuwa makaranta a Nijeriya. An fara ƙaddamar da shirin ne mai suna ‘Safe school initiatiɓe’ a ranar 7 ga Mayun 2014, don…
Read More
‘Ƴan bindiga sun kashe fararen hula sama da 35 a Gabashin Congo

‘Ƴan bindiga sun kashe fararen hula sama da 35 a Gabashin Congo

Fararen hula fiye 35 ne wasu mayaƙan ƙungiyar CODECO suka kashe, a wani hari da suka kai wasu ƙauyuka da ke lardin Ituri na Jamhuriyar Dimokaraɗiyyar Congo a daren ranar Litinin. Basaraken ƙauyen Djugu, Jean ɓianney ya ce ƴan bindigar sun kai harin ne da misalin ƙarfe 8 na daren Litinin, inda suka kashe mutane tare kuma da ƙona gidaje. Ya ce izuwa safiyar Talatar, sun gano gawarwaki sama da 35, bayaga waɗanda suka samu raunuka da kuma asarar dukiyar da aka tabka. Shugaban wata ƙungiyar farar hula a yankin Jules Tsuba, ya ce izuwa safiyar Talata, sun gano gawarwakin…
Read More
Trump ya lafta harajin kashi 25 kan ƙarafan da ake shigarwa Amurka

Trump ya lafta harajin kashi 25 kan ƙarafan da ake shigarwa Amurka

Shugaban Amurka Donald Trump ya sanar da lafta harajin kashi 25 kan ƙarafai da samfolon ko kuma Alminium da ake shigarwa ƙasar daga ƙetare ba tare da cirewa ko kuma sauƙaƙawa kowacce ƙasa ba. Harajin na Trump kan ƙarafa da Alminium ko kuma Samfolon da ake shigarwa Amurka da zai fara aiki nan take, duk da cewa kai-tsaye shugaban Chana ya nufata da shi amma zai fi illa ga ƙasashen Canada da Brazil da kuma Meɗico waɗanda sune suka fi shigar da kayan cikin Washington. A jawabinsa bayan sanar da lafta harajin, Trump ya bayyana cewa wannan muhimmin lamari ne…
Read More
Falasɗinawa za su yi farin ciki da inda za mu kai su – Trump

Falasɗinawa za su yi farin ciki da inda za mu kai su – Trump

Shugaban Amurka Donald Trump ya sake jaddada aniyarsa ta karɓe Gaza da kuma kwashe Falasɗinawan da ke wurin zuwa ƙasashen Jordan da Masar tare da wasu ƙasashen Larabawa. Yayin ganawa da Sarki Abdallah na Jordan wanda ya ziyarce shi a Washington, Trump ya ce yana da yaƙinin cewar za su samu fili a ƙasashen Jordan da Masar inda za a kai Falasɗinawan da za a kwashe daga Gazar. Shugaban ya ce bayan kammala tattaunawar da suke yi za a samu wurin da za a aje Falasɗinawan da ke Gaza da za su zauna cikin farin ciki. Yayin tsokaci akan matsayin…
Read More
Hamas ta sako fursunonin Isra’ila uku a musayar Falasɗinawa 183

Hamas ta sako fursunonin Isra’ila uku a musayar Falasɗinawa 183

A ranar Asabar ne mayaƙan Hamas ta sako ƙarin wasu fursunonin Isra’ila guda uku akan musayar Palastinawa 183 da Isra’ila ta sako a matsayin wani ɓangare na yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza. An gudanar da waƙoƙi gabannin musayar a birnin Deir Al-Balah a safiyar Asabar da jami’an bada agaji na Red Cross da wasu ƴan Hamas suka jagoranta. Jami’an Red Cross ne suka gabatar da fursunoni ukun ga sojojin Isra’ila a yankin Kudancin ƙasar inda suke karɓar kulawar lafiya a matakin farko. Wata sanarwa da hukumomin tsaro na Isra’ila suka fitar, ta ce sun yi kira ga al’umma da su…
Read More
Ƙasar Rasha ta saki wani malami Ba’amurke da take tsare da shi

Ƙasar Rasha ta saki wani malami Ba’amurke da take tsare da shi

An sako wani malami Ba’amurke, wanda aka yanke wa hukunci bisa kuskure, kuma ake tsare da shi a Rasha, Marc Fogel, a wani abin da fadar White House ta bayyana a matsayin diflomasiyya da ka iya ciyar da tattaunawar kawo ƙarshen yaƙin Ukraine. Steve Witkoff, ɗan aike na musamman daga Shugaba Donald Trump, ya bar filin saukar jirage na Rasha tare da Fogel, wani malamin tarihi daga Pennsylɓania, kuma ana sa ran zai sake haɗuwa da iyalinsa a ƙarshen wannan rana. An kama Fogel a watan Agustan 2021 kuma yana zaman gidan yari na shekaru 14. Iyalinsa da magoya bayansa…
Read More