14
Jul
Daga JAMIL GULMA a Kebbi Shugaban ƙungiyar Miyetti Allah reshen ƙaramar hukumar Argungu Alhaji Hara Akote Badariya ya bayyana ɗaukar doka a hannu ne dalilin faɗa tsakanin manoma da Fulani makiyaya.Ya yi wannan bayanin ne a wata hira da ya yi da waƙilin jaridar Blueprint Manhaja a garin Argungu.Alhaji Akote Badariya ya ce tsakanin manoma da Fulani a ƙasar nan ba wanda ke iya raba su saboda ɗaya bai yi sai da ɗaya don haka suka tarar tun kakanni da iyaye, idan makiyaya suka yi ɓarna ko dai a yi sulhu tsakanin su ba sai an je ga hukuma ba…
